Makwabtan Fatima da aka Kashe da Yaranta 6 a Kano Sun Fusata Rundunar 'Yan Sanda

Makwabtan Fatima da aka Kashe da Yaranta 6 a Kano Sun Fusata Rundunar 'Yan Sanda

  • Rundunar ’yan sandan Kano ta karyata zargin da makotan Fatima Abubakar ke yadawa a kafafen sada zumunta bayan sun gaza kai dauki har aka kashe ta da yaranta
  • Wasu hirarraki da aka yi da wasu daga cikin makwabtan na bayyana cewa da su aka taimaka wajen kama mutanen da ake zargin sun aikata kisan mutum bakwai a Chiranchi Dorayi
  • ’Yan sanda sun ce makwaba ba su kai agaji ba, kuma duk da wannan rashin taimako, sun fito bainar jama'a suna sharara karya a kan mummunan aikin da ya girgiza mutane

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano – Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta zargi makwabtan Fatima Abubakar da wasu ɓata-gari uku suka hallaka tare da yaranta da yaɗa shararar ƙarya a kafafen sada zumunta.

Kara karanta wannan

Badakalar fansho: Abdulrasheed Maina ya shaki iskar 'yanci bayan shekaru 8 a garkame

A ranar Asabar, 17 ga watan Janairu, 2026 ne wasu ɓata-garin mutane suka shiga gidan Fatima, suka kashe ta da yaranta shida, sannan aka jefa ɗaya daga cikinsu a rijiya.

Rundunar yan sanda ta ji takaicin kalaman makotan Fatima Abubakar
Umar Auwal, wanda ake zargin dan uwa ne ga Fatima Abubakar da yagoranci kashe ta da 'ya'yanta 6 a Kano. Hoto: Hussaina Abkr
Source: Facebook

A wata sanarwa, kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, ya wallafa a Facebook, ya bayyana takaicinsa game da abin da ya kira “ƙarya” da makotan Fatima ke yadawa a shafukan sada zumunta.

Bayanin makwabtan Fatima a Kano

A wani bidiyo da Aminci Radio ta wallafa a shafinta na Facebook, wasu makwabtan Fatima sun bayyana cewa ba gaskiya ba ne zargin da ake yi musu na cewa ba su kai wa matar da yaranta agaji ba.

Malam Bala Abubakar, wanda ke zaune a wurin makokin matar, ya ce sun kai ɗauki, sai dai ba su isa wurin da wuri ba saboda yadda lamarin ya faru cikin kankanin lokaci.

Yan sandan Kano sun ce makotan Fatima sun shirga karya
SP Abdullahi Haruna Kiyawa, kakakin rundunar yan sandan Kano Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Source: Facebook

Ya ce:

“Har yanzu ba mu cikin hayyacinmu muke ba saboda wannan bala’i da muka gani. Duk wanda ya ce maka a unguwar nan mutane suna barci, ƙarya yake wallahi. Kawai ihu muka ji, muka ɗauki matakin gaggawa. Amma da muka zo, sun riga sun gama yin abin da za su yi. A kankanin lokaci suka aikata laifin, sun gama shiri.”

Kara karanta wannan

Abubakar Malami ya yi magana game da makamai da DSS ta gano a 'gidansa' na Kebbi

Malam Bala ya ƙara da cewa:

“Ihu barawo ne na farko, ihu barawo na biyu, an zagaye unguwar nan.”

Ya ce yara ne suka fara jin ihun matar da yaranta, lamarin da ya kai ga kunnen makota, sannan aka yi ƙoƙarin kai musu ɗauki.

A cewarsa, makwabta sun taimaka wajen kama mutanen da ake zargi da aikata laifin tun a wurin, saboda haka ba daidai ba ne a zarge su da rashin taimakon ceton rai.

Ya jaddada cewa unguwar ta girgiza ƙwarai da abin da ya faru, kuma mutane sun shiga alhini da ba za a manta da shi cikin sauƙi ba.

Martanin rundunar ’yan sandan Kano

Wannan hira da makamantanta da suka karade kafafen sada zumunta ba su yi wa rundunar ’yan sandan Kano daɗi ba.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Kiyawa, ya zargi mutanen da nade hannaye da cewa babu wani agaji na gaske da suka kai wa matar da yaranta har aka kashe su duka.

Kara karanta wannan

An fitar da sunayen mutane 177 da 'yan bindiga suka sace suna tsakiyar ibada a Kaduna

Ya ce:

“Abin takaici ne matuƙa. Kuna cikin unguwa, kun ƙi ku taimaka, amma kun zo kafafen sada zumunta kuna ta yaɗa ƙarya.”

An shiga damuwa kan rashin tsaro a Kano

Dr. Suleiman Isyaku Muhammad, masani a fannin Ilimin Laifuka da Nazarin Tsaro a Jami’ar Tarayya ta Dutse, ya danganta tabarbarewar tsaro da rushewar tsarin tsaro na gargajiya da kuma lalacewar tsarin zamantakewar al’umma.

Ya shaida wa Legit cewa:

“Lalacewar tsarin tsaro na gargajiya a jihar Kano na taka muhimmiyar rawa wajen tabarbarewar tsaron jama’a."

Ya bayyana cewa abubuwa kamar yawaitar birane, sauyawa daga tsarin iyali mai yawa zuwa kadan, da kuma rashin ingantattun tsare-tsaren kula da unguwanni, na daga cikin dalilan da suka jawo raunin tsarin tsaro na gargajiya.

Dr. Suleiman Isyaku Muhammad ya shawarci gwamnati a kan ta karfafa wa hukumomin tsaro na unguwanni da dawo da tsarin sa ido a kan unguwannin domin kawo karshen matsalolin.

Kano: Mahaifin Umar na so a hukunta dansa

Kara karanta wannan

An cafke babban malamin Musulunci, an kai shi kotu kan cinye filaye a Kano

A baya, mun wallafa cewa Malam Auwal, mahaifin Umar da ake zargi da jagorantar kisan wata baiwar Allah mai suna Fatima Abubakar tare da dukkannin yaranta ya yi magana kan lamarin da ya girgiza al’umma.

Umar, tare da wasu mutane uku, na hannun jami’an ’yan sandan jihar Kano bayan sun amsa laifin shiga gidan Fatima Abubakar tare da kashe ta da yaranta shida a ranar Asabar, 17 ga watan Janairu, 2026.

Mahaifin Umar ya bayyana cewa ba shi da hannu, haka kuma yana cikin takaici da dimuwa a kan yadda dansa ya kashe kanwarsa da dukkanin yaranta, sannan ya nemi hukuma ta hukunta shi.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng