Ramadan: Izala Ta Fitar da Jerin Malaman da za Su Yi Tafsir a Jihohi, Kasashe a 2026

Ramadan: Izala Ta Fitar da Jerin Malaman da za Su Yi Tafsir a Jihohi, Kasashe a 2026

  • Kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Ikamatis Sunnah ta Ƙasa ta fitar da sunayen malaman da ta tura tafsirin Ramadan na 1447/2026
  • An tura malamai jihohi da dama a Najeriya da kuma wasu kasashen makwabta a Afirka ta Yamma da wasu kaashen Afrika ta Tsakiya
  • Kungiyar Izala ta ce an tsara dukkan matakan ne domin isar da ilimin Al-Kur’ani mai girma ga al’ummar Musulmi a watan Ramadan

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Filato - Kungiyar Izala karkashin jagorancin Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir ta tura malamai tafsirin Al-Kur’ani jihohi da kasashe a Ramadan 1447/2026.

Sanarwar ta fito ne daga hedkwatar kungiyar, inda ta bayyana cewa shirin yana daga cikin manyan ayyukan da JIBWIS ke gudanarwa a duk shekara domin ilmantarwa, tarbiyya da kuma yada Musulunci.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta shige gaba don shari'a kan kisan matar aure da yaranta 6

Shugaban malaman Izala, Sheikh Sani Jingir
Sheikh Sani Yahaya Jingir yayin nasihar Juma'a. Hoto: Hamza Muhammad Sani
Source: Facebook

Legit Hausa ta tattaro bayanai game da tura malamai tafsiri ne a wani sako da Hamza Muhammad Sani ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Izala ta tura malamai tafsirin Ramadan

A cewar sanarwar, shugabancin JIBWIS ya kammala dukkan tsare-tsare tun kafin shigowar watan Ramadan, domin bai wa malamai damar isa wuraren da aka tura su tafsir cikin lokaci.

Kungiyar ta bayyana cewa an rarraba malamai zuwa jihohi da dama ciki har da Plateau, Kaduna, Bauchi, Gombe, Kano, Borno, Kebbi, Sokoto da sauransu.

Haka kuma, sanarwar ta nuna cewa shirin bai tsaya a cikin Najeriya kadai ba, domin an tura wasu malamai zuwa kasashen Nijar, Burkina Faso, Ghana, Chadi, Togo, Kamaru, Mali, Benin, Cote d’Ivoire da kuma Amurka.

Jerin malaman da aka tura tafsir

1. Ash-Sheikh Muh’d Sani yahaya JINGIR da Hafiz Aminu Yusuf Nuhu, 'Yan Taya, Plateau

2. Sheikh Yusuf Muh’d Sambo da Hafiz Abdullahi Baffa Itas, Kaduna

Kara karanta wannan

Abba, Barau da hukumomi 2 da suka yi alkawarin nema wa Fatima da yaranta 6 adalci

3. Sheikh Dalhatu Abubakar Kantana da Hafiz Abdurrahman Ahmad, Gombe

4. Sheikh Nasir Abdulmuhy da Hafiza Abdulmuni Aliyu, Nasarwa

5. Bar. Aliyu Alhassa Sangei, Unguwar Rimi, Plateau

6. Dr Hassan Abubakar Dikko, Toro, Bauchi

7. Prof. Abdurrahman Lawal Adam, Jos ta Arewa, Plateau

8. Sheikh Madu Mustafa da Dr. Abubakar Musa Bako, Maiduguri, Borno

9. Sheikh Abdurrahman Isa Jega da Hafiz Muhammad Naziru Jega, Birnin Kebbi

10. Sheikh Hamza Adam Abdulhamid, Jost ta Arewa, Plateau

11. Sheikh Salihu Sulaiman Ningi da Hafiz Yusuf Shu’aibu, Ningi, Bauchi

12. Ustaz Muhammad Umar Zango Kambama da Hafiz Isma'ila Gwadangwaji, Koko, Kebbi

13. Sheikh Abubakar Usman Mabera, Sokoto

14. Mal. Abubakar Qamarawi, Ibadan, Oyo

15. M. Murtala Abubakar Imam, Keffi-Nasarawa

16. Shittiman Borno Mal. Bashir Umar Kashere, Gashua, Yobe

17. Mal. Auwal Sa'eed Jikan Mai Waina, Bus Stop, Kaduna, Kaduna

18. Ustaz Umar Hassan Gusau, Gusau, Zamfara

19. M. Haruna Ibrahim Gashua, Kumo, Gombe

20. Hafiz Aliyu Abdulwahab, Misau, Bauchi

Kara karanta wannan

Harin Amurka: An 'gano' inda 'yan ta'adda ke tserewa saboda ruwan wuta a Sokoto

21. Sheikh Khadi Abdulmumin, Jalingo, Taraba

22. M. Ibrahim Yunusa Ugo, Uguaba, Enugu

23. Ustaz Musa Abdullahi, Potiskum, Yobe

24. Sheikh Adamu Girbo, Malam Sidi, Gombe

25. Dr. Aliyu Isa Makurdi, Makurdi, Benue

26. Hon. Ustaz Muh'd Muhammad Abubakar, Magama Gumai, Toro, Bauchi

27. Dr. Mas'udu Ibrahim Tulu, Maitama, FCT Abuja

28. Mal. Muh’d Kabiru Asshikawi, Kontagora, Niger

29. Mal. Mustapha Salihu Bamalli, Guzape, FCT

30. Ustaz Yusuf Kaura Maishafi da Hafiz Nawwasi Potiskum, Zuru, Kebbi

31. M. Dawd Salahuddeen da Imam Hassan Lokoja, Kogi

32. Dr. Mal. Aliyu Rashid Makarfi, Tal’udu, Kano

33. Ustaz Ibrahim Muh'd Duguri, Jalingo, Taraba

34. M. Muhammad Sani Usman Kakiyayi, Zaria-Kaduna

35. Ustaz Iliyasu Ibrahim Maigatari, Maigatari, Jigawa

36. M. Isa Ruwan Bago, Jimeta, Adamawa

37. Hafiz Abubakar Abu Sumayya, Jama’are, Bauchi

38. M. Abbas Ahmad Aliyu-Jingre, Bassa, Plateau

39. Dr. Habibu Danbatta, Dutse, Jigawa

40. Dr. Sani Ibrahim Jalingo, Jalingo, Taraba

41. M. Musa Salihu Alburhan da Hafiz Sa'adu Dalam Tilde, Tulu, Toro, Bauchi

Kara karanta wannan

An gano gargadin da aka yi wa Donald Trump har Amurka ta fasa kai hari Iran

42. Prof. Nuhu Tahir Tajuddeen, Zaria, Kaduna

43. Dr. Aliyu Ibrahim Shafi'i, Minna, Niger

44. M. Abubakar Umar Rabo, Ganye, Adamawa

45. Mal. Muhammad Sani Bichi, Bichi, Kano

46. Dr. Bashiru Mashema da Ustaz Zaidu Sa’adu, Lagos

47. M. Abdullahi Muhammad Idris, Akure, Ondo

48. M. Muhammad Dabo Dengi, Mavo-Wase, Plateau

49. M. Muhammad Bashir Abuga, Calabar

50. Hon. Ahmad Muhammad Ashir, Bukur, Jos

51. Prof. Chika Makarantar Mai Gona, Sokoto

52. Mal. Bawa Ibrahim Kafanchan, Jama’a, Kaduna

53. Mal. Ibrahim Natalatu, Bojude, Gombe

54. M. Yusuf Mustapha Takwashe da M. Abu Sa’ad, Asaba, Delta

55. Ardo Mahmud Adam-Mahanga, Riyom, Plateau

56. Mal. Yahaya Muhammad, Lafia, Nasarawa

57. Mal. Yakubu Hussaini, New Bussa, Niger

58. Mal. Idris Ardo Lere, G/Kurama, Lere, Kaduna

59. Dr. Idris Sulaiman Minna, Nasarawa

60. M. Ahmad Salihu Bukar-Y/Shendam, Plateau

61. Mal. Yusuf Sa'eedu Kirki, Dengi-Kanam, Plateau

62. Mal. Shu'aibu Almadani, Kwaya-kusar, Borno

63. Mal. Aliyu Wase, Gombi, Adamawa

64. Mal. Muhammad Idris, Kashere, Gombe

Kara karanta wannan

Zafin siyasa bai hana aiki: Abba ya fadi shirin gwamnati a kan matasa 50, 000 a Kano

65. M. Zubairu Muhammad Fari Gire, Mubi, Adamawa

66. Mal. Sunusi Dahir Mukhtar, Zaki Biam, Benue

67. Mal. Ishaq Muh’d Jangwa, Katsina

68. Mal. Muhammad Sani Gombe, Darazo, Bauchi

69. Mal. Abubakar Yusuf Yawuri, Yawuri, Kebbi

70. M. Adam Muhammad Gadar Sogai da Hafiz Zubairu Adam Ibrahim Maishafi, Bauchi

71. M. Muhammad Salihu Imam, Bayelsa

72. M. Mukhtar Aliyu Yabo, Nakasari, Sokoto

73. M. Shitu Saharanu, Tambuwal, Sokoto

74. SP. Ahmad Adam Kutubi, Wuse Zone (3)-FCT-

75. Dr. Jibrin Abdullahi, Akwanga, Nasarawa

76. M. Nasir Hussaini Bayero, Dawaki AMAC, FCT

77. Imam Jafar Hussain, Tsando, Gombe

78. Ustaz Abubakar Salihu Zaria, Damaturu, Yobe

79. Ustaz Babangida Muhammad, Azare, Bauchi

80. Mal. Haruna Y/Shendam, Mangu, Plateau

81. Mal. Aliyu Muhammad Bara, Deba, Gombe

82. Mal. Idris Sarkin Hausawa, Zungeru, Niger

83. Ustaz Abdussalami Abubakar Jega da Hafiz Mustapha Dahir Isa, Niamey, Niger

84. M. Muh'd Rabi'u Adam, Hiro, Niger

85. M. Sulaiman Mamman, Yamai, Niger

86. Sheikh Dr. Kindo Muhammad, Burkina Faso

Kara karanta wannan

AFCON 2025: Abin da muka sani game da Laryea, alkalin wasan Najeriya da Morocco

87. Sheikh Abubakar Wadrago, Burkina Faso

88. M. Abdullahi Atibobo, Ghana

89. M. Juma'a Adam, Chad

90. Sheikh Dr. Yahaya, Chad

91. M. Abdullahi Abdullahi, Chad

92. M. Hussaini Muh'd Sankensi, Togo

93. Sheikh Abdullahi Imam, Togo

94. Sheikh Zakariyya Imam, Togo

95. Mal. Bako Abubakar, Cameroon

96. Imam Muhammad Auwal, Cameroon

97. M. Muhammad Taraware, Mali

98. M. Abubakar Kamaru, Mali

99. M. Umar Jaho, Mali

100. M. Ahmad Muhammad, C/Africa

101. Sheikh Abdussalami, Code'I'voire

102. Sheikh Dr. Dawud Kandi, Benin

103. Sheikh Mustafa, Benin.

104. Sheikh Ibrahim, Benin

105. Sheikh Ahmed Imam, New York, America

Shugaban Izala na kasa, Sheikh Sani Yahaya Jingir
Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir. Hoto: Hamza Muhammad Sani
Source: Facebook

Sheikh Habibu Yahaya Kaura ya rasu

A wani labarin, mun kawo muku cewa an sanar da rasuwar babban malamin Izala, Sheikh Habibu Yahaya Kaura a birnin tarayya Abuja.

Sheikh Ibrahim Aliyu Kaduna ne ya sanar da rasuwar malamin, inda ya ce sun rasa uba tare da fatan Allah ya gafarta wa marigayin.

Malamai da dama da suka hada da Sheikh Mansur Sokoto da Dr Jabir Sani Mai Hula sun yi maganganu game da rasuwar malamin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng