Tashin Hankali: Mutum Ɗauke da Adda Ya Tarwatsa Masu Ibada, Ya Ce Ana Damunsa

Tashin Hankali: Mutum Ɗauke da Adda Ya Tarwatsa Masu Ibada, Ya Ce Ana Damunsa

  • Wani bidiyo ya bazu inda aka ga wani mutum dauke da adda ya kutsa cocin yana korafin damunsa da ake yi
  • Mutumin ya umurci masu ibada su fita daga cocin yayin da suke kokarin kwantar masa da hankali, hakan ya janyo muhawara a kafafen sada zumunta
  • Daga masu tir da shi sai wasu da suka goyi bayan korafinsa kan gurbatar muhalli da hayaniya daga coci a unguwanni

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Umuahia, Abia - An shiga firgici a jihar Abia bayan wani mutumi dauke da adda ya shiga coci cikin bacin rai saboda yawan damunsa da ake yi

Ra’ayoyi masu zafi sun biyo bayan bidiyon da ya yadu, inda aka ce wani mutum ya shiga coci yana yin barazana ga masu ibada.

Wani ya fusata kan hayaniya daga coci, ya tarwatsa su
Taswirar jihar Abia da ke da kaso mafi yawa na Kiristoci. Hoto: Legit.
Source: Original

A bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta da Punch ta gano, an ga mutumin tsaye a cikin cocin yana umartar masu ibada su fice.

Kara karanta wannan

Mutanen Dorayi sun fadi ainihin abin da ya faru kan kisan Fatima da yaranta 6 a Kano

Yadda kararrakin coci ke damun mutane

Irin wannan kara daga wuraren ibadu da dama ya sa wasu gwamnatoci ke sanya doka domin daidaita sautuka da ke fita daga coci-coci.

A shekarar 2024, gwamnatin Lagos ta kakaba doka da ta tanadi cin tara da hukunci mai tsanani kan wadanda suka saba doka.

Mutumi da makami ya watsa masu ibada

Lamarin ya faru ne a Ibeku da ke birnin Umuahia, jihar Abia inda mutumin dauke da adda ya ce ana damunsa.

An gano wasu daga cikin mambobin cocin har da dattawa na kokarin kwantar masa da hankali da rarrashinsa.

Lamarin ya jawo muhawara a shafukan sada zumunta inda jama’a ke bayyana ra’ayoyi daban-daban kan matsalar hayaniya daga wuraren ibada a unguwanni.

Wani mai amfani da X, @ChuksEricE shi ma ya wallafa bidiyon a shafinsa inda ya ce lamarin bai yi dadi ba ko kada.

A cikin rubutunsa, ya ce:

"Wani mutum ya tayar da tarzoma a wani shirin taron daren addu’a na coci da addaba, sakamakon korafin hayaniya, a Ibeku, Umuahia, Jihar Abia."

Kara karanta wannan

'Wanda aka kashe matarsa da 'ya'yansa 6 a Kano na bukatar taimako'

Wani ya tarwatsa masu ibada a coci
Dakin ibada na Kiristoci da ake kira coci. Hoto: Legit
Source: Getty Images

Mutane sun bayyana ra'ayoyinsu

Mutane da dama suka ce hayaniya ba daidai ba ce, amma sun soki ‘yan cocin saboda barin mutumin ya shigo dauke da makami ba tare da taka masa birki ba.

Wata mai sharhi ta ce ko da ba hanya ce mai kyau ba, watakila mutumin ya bi hanyoyin doka amma babu wanda ya saurare shi har ya kasa hakuri.

Wasu sun ce cocin na iya fuskantar shari’a saboda rashin sanya ka'ida na sauti, inda suka jaddada cewa hayaniyar coci-coci na Pentecostal na damun mazauna yankuna da dama.

Wani ya yanka ladanin masallaci a Kano

A baya, kun ji cewa al’ummar Hotoro Maraba a Kano sun shiga firgici bayan wani matashi ya kashe ladanin masallaci a lokacin sallar Asubahi.

Rahotanni sun ce rikici ya fara ne bayan ladani ya ce lokacin sallah bai yi ba, lamarin da ya fusata matashin ya yanke makogoronsa.

'Yan sanda sun dauki mataki a yankin domin hana barkewar tarzoma bayan fusatattun matasa sun yi kukan kura sun kashe matashin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.