Shugaba Tinubu Ya Bada Umarni game da Kisan Matar Aure da Yaranta 7 a Kano

Shugaba Tinubu Ya Bada Umarni game da Kisan Matar Aure da Yaranta 7 a Kano

  • Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa Fatima Abubakar da yaranta shida a unguwar Chiranci dake Kano
  • Shugaban kasar ya ba da 'yan sanda sabon umarni yayin da aka ce an kama mutane uku da ake zargi da aikata wannan danyen aikin
  • Shugaba Tinubu ya kuma jajanta wa al'ummar jihar Kano bisa rasuwar babban dan kasuwa Alhaji Bature Abdulaziz a karshen mako

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nuna tsananin damuwarsa tare da yin Allah-wadai da kisan gilla da aka yi wa Fatima Abubakar da yaranta shida.

Wannan danyen aiki ya faru ne a unguwar Chiranci dake cikin birnin Kano, inda mahara suka shiga cikin gidan Fatima, suka kashe ta da dukkan 'ya'yanta.w

Kara karanta wannan

'Wanda aka kashe matarsa da 'ya'yansa 6 a Kano na bukatar taimako'

Shugaba Bola Tinubu ya yi alhinin kisan Fatima da yaranta 6 a Kano
Shugaba Bola Tinubu a lokacin da zai jagoranci taron FEC a Abuja. Hoto: @DOlusegun
Source: Twitter

Umarnin Tinubu kan kisan matar aure

A wata sanarwa da Bayo Onanuga, ya fitar, kuma Olusegun Dada ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin, Tinubu ya bayyana kisan a matsayin wani aiki na rashin imani.

Shugaban kasar ya jinjina wa rundunar yan sanda bisa yadda suka yi gaggawar kamo mutane uku da ake zargi da aikata wannan danyen aiki.

Tinubu ya bayyana cewa:

"Ina jinjina wa yan sanda kan kamo manyan wadanda ake zargi, kuma na bada umarnin a gudanar da sahihin bincike akansu."

Ya ci gaba da cewa:

"Dole ne a tabbatar da cewa an gurfanar da wadannan mutane gaban kotu domin su fuskanci hukuncin da ya dace da laifinsu."

Bayanan rundunar yan sandan jihar Kano

Kafin jawabin shugaban kasar, rundunar 'yan sandan Jihar Kano ta sanar da kama wadanda ake zargin tsakanin daren 17 da asubar 18 ga Janairu, 2025.

Kara karanta wannan

Mahaifin Umar ya barranta da 'dansa da ake zargi da kashe yar uwarsa da yara 7

CSP Abdullahi Kiyawa ya bayyana cewa daya daga cikin wadanda aka kama, wanda dan uwan marigayiyar ne, ya amsa laifin kulla wannan kisan gilla.

Legit Hausa ta rahoto mai magana da yawun 'yan sanda ya ce:

"Babban wanda ake zargin ya amsa laifin, sannan ya tabbatar da cewa kungiyarsu ce ke kai hare-hare a sassan birnin Kano daban-daban."
Shugaba Bola Tinubu ya yi ta'aziyyar dan kasuwar Kano da ya rasu
Shugaba Bola Tinubu yana gabatar da addu'o'i a cikin masallacin kasa, Abuja. Hoto: @DOlusegun
Source: Facebook

Ta'aziyyar rasuwar babban dan kasuwar Kano

Haka kuma, Shugaba Tinubu ya bayyana alhini kan rasuwar fitaccen dan kasuwar nan na Kano, Alhaji Bature Abdulaziz, wanda ya rasu a karshen makon nan.

Shugaban kasar ya bayyana rasuwar tasa a matsayin babban rashi ga daukacin harkar kasuwanci a Najeriya, ba wai ga jihar Kano kadai ba baki daya.

Sanarwar Onanuga ta rahoto Tinubu yana cewa:

"Marigayi Bature Abdulaziz ya kasance jajirtaccen shugaba wanda ya ba mu gagarumin goyon baya a lokacin yakin neman zabenmu na shekarar 2023."

An ce marigayi Dr. Bature Abdulaziz shi ne shugaban kungiyar hadakar yan kasuwa ta Najeriya, sannan kuma ya kafa kungiyar dattijai masu kishin kasa domin zaman lafiya.

Kara karanta wannan

Tazarce: Gwamna ya jero dalilan da za su sanya ƴan Kaduna su zabi Tinubu a 2027

Kano: Mijin Fatima na bukatar taimako

A wani labari, mun ruwaito cewa, al’umma sun fara kira da a hada kai domin taimakawa Malam Bashir Haruna, da aka kashe 'ya'yansa shida da matarsa a Kano.

Barista Abba Hikima ya bayyana jerin abubuwan da ya ce ya kamata a masa da nufin saukaka radadin da mutumin ke ciki tare da farfado da rayuwarsa.

Masu ruwa da tsaki sun bukaci gwamnati, attajirai da ’yan jarida su nuna tausayi a mu’amalarsu da wanda abin ya shafa lura da halin da yake ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com