Fasto Kukah Ya Yi Amai Ya Lashe kan Zargin Kisan Kiristoci, Ya Tabo Musulmai

Fasto Kukah Ya Yi Amai Ya Lashe kan Zargin Kisan Kiristoci, Ya Tabo Musulmai

  • Fasto Matthew Kukah ya yi martani game da rahotannin da ke cewa ya taɓa faɗin babu kisan Kiristoci a Najeriya
  • Kukah ya ce an karkatar da kalamansa, yana jaddada cewa ana kashe Kiristoci kuma hakan bai kamata ya faru ba
  • Limamin ya bayyana cewa matsalar tsaro na shafar duk ’yan Najeriya, Musulmi da Kiristoci ba tare da bambanci ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Fasto Matthew Kukah, na Cocin Katolika a Sokoto ya kuma yin magana game da zargin kisan Kiristoci a Najeriya.

Mathew Kukah ya musanta rahotannin da ke cewa ya taɓa faɗin cewa babu tsananta wa ko gallaza wa Kiristoci a Najeriya.

Fasto ya yi karin haske kan zargin kisan Kiristoci a Najeriya
Shugaba Bola Tinubu da Fasto Matthew Hassan Kukah. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Kukah ya yi wannan bayani ne yayin da ya halarci wani shirin rediyo mai suna 'Boiling Point', wanda jaridar Punch ta bibiya.

Kara karanta wannan

Jigon ADC ya zargi Tinubu da sakaci, an tsunduma mutane miliyan 141 a bakin talauci

Donald Trump ya yi barazana ga Najeriya

A ranar 31 ga Oktobar 2025, Shugaban Amurka Donald Trump ya sake sanya Najeriya a jerin ƙasashen da ake kira CPC sakamakon zarge-zargen cewa ana aiwatar da kisan kiyashi ga Kiristoci a ƙasar.

Kalmar CPC dai tana nufin ƙasa da ake zargi da take ’yancin addini da ke ci gaba da faruwa ba tare da katsewa ba. Gwamnatin Najeriya ta sha musanta zargin kisan kiyashi ga Kiristoci.

A ranar 25 ga Disambar 2025, Amurka ta kai hare-haren sama kan wasu sansanonin ’yan ta’adda biyu a dajin Bauni, da ke ƙaramar hukumar Tangaza a Jihar Sokoto.

Amurka ta kawo hari Najeriya kan zargin kisan Kiristoci
Shugaba Bola Tinubu da Donald Trump na Amurka. Hoto: Bayo Onanuga, Donald J Trump.
Source: Twitter

Kukah ya musanta cewa ba a kashe Kiristoci

Yayin martanin, Kukah ya ce an karkatar da kalamansa game da zargin kisan kiyashi ko tsanantawa ga Kiristoci a ƙasar.

Sai dai ya ce ba a fahimci maganarsa ba kuma bai son komawa baya amma dai kowane addini ka ke za a iya sace ka a Najeriya, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

Amurka ta yi barazana, za a lafta haraji a kan kasashen da ke mu'amala da Iran

Da yake magana kan cece-ku-cen, Kukah ya ce:

“Ban taɓa musanta cewa ana kashe mutanenmu (Kiristoci) ba. Abin da aka rika faɗa game da kalamaina ya ba ni mamaki sosai.
“Ko kisan kiyashi ko musgunawa wallahi wannan abu bai kamata ya faru ba. Duk inda za mu samu taimako, ko daga Trump ko wani, dole ne a hana waɗannan kashe-kashe.”

Kukah ya jaddada cewa matsalar rashin tsaro a Najeriya ba ta taɓa bambanta addini ba, yana mai cewa Musulmi da Kiristoci duk suna fuskantar barazanar sace-sace da hare-hare.

“Ko Musulmi ne, ko Kirista, kowa na cikin haɗarin sacewa a Najeriya."

- In ji Kukah

Fasto Kukah ya shawarci Tinubu kan tsaro

Kun ji cewa Fasto Mathew Kukah ya ce Najeriya ba za ta iya kawo ƙarshen ta'addanci da karfin soja kaɗai ba, domin bindiga ba ta kawar da akida.

Malamin cocin ya yi kira da a rungumi sulhu, shugabanci nagari, da adalci domin magance tushen rashin tsaro da tashe tashen hankula.

Ya gargadi Shugaba Bola Tinubu cewa ci gaban tsaro da ake gani a yanzu na wucin gadi ne, ba wai an kawo karshen matsalar kenan ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.