Wata Sabuwa: Kotu Ta Kwace Kadarori 57 na Malami a Kano, Abuja da Wasu Jihohi 2

Wata Sabuwa: Kotu Ta Kwace Kadarori 57 na Malami a Kano, Abuja da Wasu Jihohi 2

  • Wata Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta ba da umarnin wucin gadi na kwace wasu kadarori da ake zargin na Abubakar Malami ne
  • Mai shari'a Emeka Nwite ya ba da wa'adin kwanaki 14 ga duk wanda ke da hujjar mallakar dukiyoyin kafin kwace kadarorin gaba daya
  • Wannan na zuwa ke bayan kotun ta ba da belin Malami da sauran wadanda ake tuhuma kan Naira biliyan 1.5 da sharudda masu tsauri

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin wucin gadi na ƙwace kadarori 57 da ake zargin suna da alaka da tsohon Antoni Janar na Tarayya (AGF), Abubakar Malami, SAN.

Hukumar EFCC ce ta shigar da bukatar kwace kadarorin bisa zargin cewa Malami, tsohon ministan shari'a ya mallake su ta hanyar amfani da kudin haram.

Kara karanta wannan

Kotu ta ba Abubakar Malami, matarsa da dansa beli, za su biya N1.5bn

Abubakar Malami.
Tsohon Antoni Janar na Tarayya, Abubakar Malami (SAN) Hoto: Abubakar Malami
Source: Facebook

Kotu ta amince da bukatar hukumar EFCC

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da umarnin a ranar Talata, yayin da yake yanke hukunci kan wata buƙatar gaggawa da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar, cewar The Nation.

Lauyan hukumar EFCC, Ekele Iheanacho (SAN) ne ya gabatar da bukatar a babbar kotun tarayya kuma ya samu nasarar amincewar mai shari’a Emeka Nwite.

Kwafin umarnin kotun da aka samu a ranar Laraba ya nuna cewa kadarorin da suka kunshi filaye da gine-ginen da abin ya shafa suna a Abuja, Kebbi, Kano da Kaduna.

Wannan na zuwa ne bayan kotun ta amince da bukatar belin Malami, 'dansa da kuma 'daya daga cikin matansa, wadanda EFCC ta gurfanar kan zarge-zargen sama da fadi da dukiyar kasa.

Kotu ta gindaya wa'adin makonni 2

A cikin hukuncin da kotun ta yanke game da batun kadarorin, Mai shari’a Nwite ya ce:

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya kare kansa bayan zargin batan N128bn a hannunsa

“Kotu ta bayar da umarnin wucin-gadi na ƙwace kadarorin da aka lissafo a jadawali na daya da ke ƙasa, waɗanda ake da hujjar cewa an same su ne ta haramtacciyar hanya."

Alkalin ya kuma umarci EFCC da ta wallafa umarnin ƙwace kadarori a jarida ta ƙasa, domin duk wanda ke da ta cewa lo ikirarin mallakar wadannan kadarorin ya gabatar da kansa cikin kwanaki 14.

Abubakar Malamai.
Tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami (SAN) tare da jami'an EFCC a cikin kotu Hoto: EFCC Nigeria
Source: Twitter

Alkalin ya bada wa'adin kwanaki 14 ga duk wanda ke ganin hukuncin bai dace ba domin ya gabatar dalilin da ya sa ba za a ƙwace kadarorin gaba daya, a mallaka wa Gwamnatin Tarayya.

Daga bisani, alkalin ya ɗage shari’ar zuwa ranar 27 ga Janairu, domin EFCC ta ba kotu rahoto kan yadda ta bi umarnin wallafa hukuncin a jarida, kamar yadda Punch ta ruwaito.

An amince da bukatar belin Malami a kotu

A wani labarin, kun ji cewa Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta amince da bayar da beli ga tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami da matarsa da dansa.

Alkalin kotun, Mai shari’a Emeka Nwite, ya ce kowanne daga cikin wadanda ake tuhuma zai bayar da Naira miliyan 500 a matsayin beli.

Kotun ta ce za su ci gaba da kasancewa a tsare har sai sun kammala cika dukkan sharudan belin da aka shimfida musu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262