Karfin Hali: An Cafke Ɓarawo bayan Sace Motar Masarautar Bauchi

Karfin Hali: An Cafke Ɓarawo bayan Sace Motar Masarautar Bauchi

  • Rundunar ‘yan sandan Bauchi ta dakile yunkurin satar motar Toyota Hilux mallakar Majalisar Masarautar Bauchi
  • Rahoton ya nuna cewa barawon ya sace motar ne a gidan mai na Inkiya yayin da direban ya tsaya sayen mai
  • ‘Yan sanda sun cafke wanda ake zargi a yankin Bayan Gari tare da kwato motar da ya yi yunkurin tserewa da ita

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Bauchi - Rundunar ‘yan sanda ta yi nasarar cafke wani da ake zargin ya sace motar masarautar jihar Bauchi.

'Yan sanda sun dakile yunkurin satar motar kirar Toyota Hilux mallakar Majalisar Masarautar Bauchi a cikin birnin Bauchi.

Yan sandan Bauchi sun kama barawon mota
Kakakin yan sanda a Bauchi, SP Nafiu Habib. Hoto: Nigeria Police Force Bauchi State Command.
Source: Facebook

An cafke barawon motar masarautar Bauchi

Hakan na cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin Facebook a jiya Talata 6 ga watan Janairun shekarar 2025.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu zai tsaya takarar gwamnan Neja a 2027? Mohammed Idris ya magantu

Lamarin ya faru ne a ranar 5 ga Janairu, 2026, lokacin da Buhari Musa Umar, mamba a Majalisar Masarautar Bauchi, ya kai rahoton satar motar, cewar Leadership.

Buhari Musa ya sanar da tawagar sintirin ‘yan sanda da ke bakin shataletale kan hanyar Jos cewa an sace motar ne yayin da direba ya tsaya a gidan mai.

Rahoton ya ce an ajiye motar Toyota Hilux a gidan mai na Inkiya yayin da direban ya tsaya sayen fetur domin ci gaba da tafiya.

Direban ya bayyana cewa yana kan hanyar domin isar da sako ne zuwa karamar hukumar Ganjuwa domin kai aika daga Mai Martaba Sarkin Bauchi.

Ya ce bayan ya sauka domin shiga banɗaki na ɗan lokaci, wani mutum ya yi amfani da damar, ya tuka motar ya tsere.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Habib, ya fitar ranar Talata 6 ga watan Janairun 2026, ya ce jami’ai sun dauki matakin gaggawa.

SP Habib ya bayyana cewa jami’an sun bi sawun wanda ake zargi tare da samun nasarar kwato motar a yankin Bayan Gari.

Kara karanta wannan

'Babu wani mahaluki': Atiku ya magantu kan janye takarar shugaban kasa a 2027

Ya kara da cewa an cafke wanda ake zargin a wurin tare da kwato motar Toyota Hilux da aka sace ba tare da wata matsala ba.

An fara binciken barawon motar masarautar Bauchi
Taswirar jihar Bauchi da aka cafke barawon mota. Hoto: Legit.
Source: Original

Alkawarin da 'yan sanda suka yi a Bauchi

Kakakin rundunar yan sanda ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin satar motar yayin da ake masa tambayoyi a ofishin ‘yan sanda.

SP Habib ya ce bincike na ci gaba, kuma ya tabbatar da cewa bayan kammala binciken za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu.

Ya ce:

"Ana ci gaba da bincike wanda da zarar an kammala masa tambayoyi za a tura shi kotu."

A halin da ake ciki, Kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya jaddada kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyi.

Ya ce rundunar za ta ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da zaman lafiya da kuma sanya jihar Bauchi ta kasance mai aminci ga kowa.

Bauchi: Matashi ya mutu a rikicin radin suna

Mun ba ku labarin cewa wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna, ya rasu bayan rikici ya ɓarke a wajen bikin suna a Jihar Bauchi.

Kara karanta wannan

Mummunar gobara ta tashi a ofishin ƴan sanda, ɗakin ajiye makamai ya ci wuta

Rikicin ya samo asali ne daga sabani da ya shiga tsakanin wasu matasa da suka halarci taron raɗin sunan.

Da farko matashin ya suma bayan rikici ya yi zafi, kafin a garzaya da shi zuwa wurin kwararru inda aka ce ya rasu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.