'Yan Ta'addan Boko Haram Sun Yi Ta'asa bayan Kai Hare Hare a Kauyukan Adamawa

'Yan Ta'addan Boko Haram Sun Yi Ta'asa bayan Kai Hare Hare a Kauyukan Adamawa

  • 'Yan ta'addan Boko Haram sun kai hare-haren ta'addanci a wasu kauyukan jihar Adamawa da ke yankin Arewa maso Gabas
  • Tsagerun 'yan ta'addan sun hallaka bayin Allah tare da kona gidajen mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba a karamar hukumar Hong
  • Majiyoyi sun bayyana cewa ba a san adadin mutanen da aka kashe ba yayin hare-haren amma an gano gawarwaki har guda takwas

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Adamawa - Wasu da ake zargin ’yan Boko Haram ne sun kashe mutane yayin wasu hare-haren ta'addanci da suka kai a jihar Adamawa.

'Yan ta'addan na Boko Haram sun kashe mutane takwas a wasu kauyuka uku da ke karamar hukumar Hong ta jihar Adamawa.

'Yan Boko Haram sun kai hari a Adamawa
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri Hoto: @GovernorAUF
Source: Facebook

Jaridar Daily Trust ta kawo rahoto cewa majiyoyin cikin gida sun tabbatar da cewa harin ya auku ne a daren ranar Litinin, 29 ga watan Disamban 2025.

Kara karanta wannan

Fusatattun mutane sun farmaki ofishin hukumar NSCDC a Kano, an rasa rayuka

'Yan Boko Haram sun kashe mutane

Bayan hare-haren an gano gawarwakin mutane takwas, yayin da mutane hudu har yanzu ba a san inda suke ba, rahoton jaridar Leadership ya tabbatar da hakan.

Wata majiya, da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce maharan sun kai hare-haren ne a kauyukan Zah, Kijing da Mubang, tana mai cewa lamarin ya kara tayar da hankalin jama’a da rashin tsaro a yankin, musamman a wannan lokacin bukukuwan Kirsimeti.

"Mutane da dama na ganin cewa adadin wadanda aka kashe ya fi takwas, domin an lalata gidaje da dama a yayin harin da aka kai daren ranar Litinin."
"Mutane da yawa sun gudu daga gidajensu domin tsira da rayukansu."

- Wata majiya

An gano gawawwaki 8 - Karamar hukumar Hong

Sai dai shugaban karamar hukumar Hong, Hon. Inuwa Usman Wa’aganda, ya ce abin da zai iya tabbatarwa a halin yanzu shi ne gano gawarwakin mutane takwas daga kauyukan da lamarin ya shafa.

Kara karanta wannan

Hankula sun tashi bayan 'yan bindiga sun kai kazamin hari a Kebbi

"Eh gaskiya ne. Boko Haram sun kai hari kauyukan Mubang, Zah da Kijing da ke karamar hukumar Hong. A halin yanzu, an gano gawarwaki takwas daga wadannan kauyuka uku, kuma mutane hudu har yanzu ba a same su ba."

- Hon. Inuwa Usman Wa'aganda

Za a iya tunawa cewa a baya ma an ruwaito hare-hare a yankunan Mayo Ladde da Garaha da ke makwabtaka da yankin.

'Yan ta'addan Boko Haram sun kai hare-hare a Adamawa
Taswirar jihar Adamawa, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta wasu labaran kan kungiyar Boko Haram

Sojoji sun ragargaji 'yan Boko Haram

A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojojin Najeriya na rundunar Operation Hadin Kai sun ragargaji 'yan ta'addan Boko Haram a jihar Borno.

Dakarun sojojin sun samu gagarumar nasara bayan da suka kai hare-haren sama a karamar hukumar Bama ta jihar Borno, inda suka samu gagarumar nasara a kan mayakan Boko Haram.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa hare-haren sun yi sanadiyyar kawar da wasu manyan kwamandojin kungiyar Boko Haram da ake dade ana nema ruwa a jallo a yankin.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng