Garkuwa da Mutane: Sojojin Najeriya Sun Gwabza Kazamin Dada 'Yan Bindiga a Kano

Garkuwa da Mutane: Sojojin Najeriya Sun Gwabza Kazamin Dada 'Yan Bindiga a Kano

  • Dakarun soji sun ceto Rabiu Alhaji Halilu tare da fatattakar 'yan bindiga bayan wani kazamin artabu a iyakar jihohin Kano da Katsina
  • Rundunar sojojin ta Brigade 3 Kano ta bayyana cewa an kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri na motsin 'yan bindiga
  • Hakazalika, dakarun Operation Hadin Kai ta kashe 'yan ta'adda 438 tare da kwace na'urorin sadarwa na Starlink guda 300

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - Dakarun hadin gwiwa na JTF da ke Faruruwa sun ceto wani mutum da aka sace bayan nasarar wani sumame na tsaro da suka kai a kan iyakar Kano–Katsina da safiyar Lahadi.

Rundunar sojojin Najeriya ta Brigade 3 Kano ta bayyana cewa an kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri na motsin 'yan bindiga a yankunan Daurawa da ke Kira zuwa Kano.

Kara karanta wannan

Malam Nata'ala da wasu fitattun jaruman Kannywood da suka rasu a 2025

Sojoji sun fafata da masu garkuwa da mutane a Kano
Sojojin Najeriya masu sintirin yaki da 'yan ta'adda. Hoto: @HQNigerianArmy
Source: Twitter

Sojoji sun fafata da 'yan bindiga a Kano

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar sojin Najeriya ta Brigade ta 3, Kano, Manjo Zubair Babatunde, ya bayyana hakan ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN).

A cewarsa, dakarun da ke aiki daga Forward Operating Base (FOB) Yankwada sun gaggauta hada rundunar sintiri domin tare hanyar ‘yan bindigar a gefen iyakar Kano da Katsina.

“Da isarsu yankin Ungwan Dogo/Ungwan Tudu, dakarun sun yi artabu da ‘yan bindigar tare da fafatawa a wata mummunar musayar wuta.
“An rinjayi ‘yan bindigar tare da tilasta musu tserewa cikin rudani zuwa Karamar Hukumar Matazu ta jihar Katsina,” in ji shi.

Manjo Babatunde ya ce a yayin artabun, dakarun sun yi nasarar ceto wani da aka sace mai suna Rabiu Alhaji Halilu, mai shekaru 38.

'Yan bindiga sun tsere zuwa cikin Katsina

Ya bayyana cewa Halilu ya samu raunin harbin bindiga a ƙafarsa a lokacin da yake hannun ‘yan bindigar, inda aka gaggauta kai shi Cibiyar Lafiya ta JTF Faruruwa, inda a halin yanzu yake karɓar magani.

Kara karanta wannan

Sulhu ya yi rana: 'Yan bindiga sun sako mutanen da suka sace a Katsina

Abubuwan da aka kwato a wajen sun haɗa da babura uku da ‘yan bindigar suka bari yayin tserewarsu, da kuma adadin shanu da ba a bayyana yawansu ba, waɗanda ake zargin sun sato su ne.

Ya ƙara da cewa dakarun sun ƙara zafafa tsaro da sintiri a yankin domin hana sake aikata laifuka da tabbatar da dorewar tsaro a al’ummomin kan iyaka.

A wani labarin kuma, ci gaba da kai farmaki da dakarun hadin gwiwa na Arewa maso Gabas, Operation Hadin Kai (OPHK) ke yi na ci gaba da haifar da gagarumar nasara.

Dakarun sojoji sun fafata da masu garkuwa da mutane a Kano
Sojojin Najeriya sun ceto wani mutumi da aka yi garkuwa da shin a Kano. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Ayyukan sojoji a Arewa maso Gabas

Rahotan da Zagazola Makama ya wallafa a shafinsa na X, sun nuna cewa ba ƙasa da ‘yan ta’adda 438 na Boko Haram da ISWAP aka kashe cikin tsawon watanni bakwai.

Kwamandan rundunar ayyuka ta OPHK, Arewa maso Gabas Sashi na 1, Manjo Janar Abdulsalam Abubakar, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar a Maiduguri, yayin liyafar Kirsimeti ta shekarar 2025 da aka shirya wa dakarun da ke fagen daga.

A cewarsa, a wannan lokaci an kwato makamai iri-iri guda 254, da kuma kusan na’urorin sadarwa na Starlink 300, waɗanda ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen inganta umarni, kulawa da tattara bayanan sirri.

Kara karanta wannan

Rawar da sojojin Najeriya suka taka yayin harin Amurka a Sokoto

Ya ƙara da cewa dakarun sun kuma ceto fararen hula 366, ciki har da mata da yara, daga maboyar ‘yan ta’adda daban-daban a yankin Arewa Maso Gabas.

'Yan sanda sun fafata da 'yan bindiga

A wani labarin, mun ruwaito cewa, 'yan sandan sun ceto Geoffrey Akume, wani mutumi da masu garkuwa da mutane suka sace a ranar Kirsimeti a Benue.

Kakakin rundunar, DSP Udeme Edet, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis, wadda aka bai wa manema labarai a Makurdi.

Ta bayyana cewa wanda aka ceto yana kan hanyarsa daga Gboko zuwa Makurdi lokacin da wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka tare shi a Tiortu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com