Tsaro ne kan Gaba da Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kudin 2026 a Majalisa

Tsaro ne kan Gaba da Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kudin 2026 a Majalisa

  • Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kudin 2026 a zaman hadin gwiwa na Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai yau Juma'a
  • Shugaban kasar ya yi bayani dalla-dalla kan yadda Najeriya za ta kashe sama da Naira tiriliyan 58 a shekara mai zuwa watau 2026
  • Bangaren tsaro shi ne ya fi samun kaso mafi tsoka a kasafin kudin, wanda aka ware sama da Naira tiriliyan 15 don biyan basussuka

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Kamar yadda aka tsara, Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kudin shekarar 2026 ga Majalisar Tarayya a Abuja.

Kara karanta wannan

Kakakin Majalisa na neman haddasa rigima a jam'iyyar APC kan tikitin zaben 2027

Bola Tinubu ya gabatar da kasafin 2026, wanda ake sa ran zai lakuma Naira tiriliyan 58.18 a gaban zaman hadin guiwa tsakanin Majalisar Dattawa da ta Wakilai yau Juma'a.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu yayin gabatar da kasafin kudi a zauren Majalisa Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

Fadar shugaban kasa ta tabbatar da hakan a wata sanarwa da mai taimakawa Tinubu kan harkokin soshiyal midiya, Dada Olusegun ya wallafa a shafin X.

Najeriya za ta kashe N58.18trn a 2026

Shugaban kasar ya bayyana cewa an ware Naira tiriliyan 26.08 domin gudanar da ayyukan ci gaba, yayin da aka ware Naira tiriliyan 15.25 a matsayin kudin tafiyar da gwamnati na yau da kullum

Mai girma Bola Tinubu ya ce an kuma sa farashin man fetur a Dala $64.85 kan kowace ganga, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

Tinubu ya ce gwamnati na sa ran samun jimillar kuɗaɗen shiga Naira tiriliyan 34.33 a shekarar 2025, sannan ta tsara kashe kuɗaɗen da suka kai Naira tiriliyan 58.18.

Daga cikin wadannan kudade, Shugaba Tinubu ya ce an ware Naira tiriliyan 15.52 domin biyan wasu daga cikin basussukan da ake bin Najeriya.

Kara karanta wannan

NLC: Ajaero ya fadi sabon alkawarin da Tinubu ya dauka game da rashin tsaro

"Za a samu gibin ₦23.85trn a kasafin kudin 2026, wanda ke wakiltar kashi 4.28 cikin 100 na karfin tattalin arziki watau GDP," in ji shi.

An gina kasafin ne bisa hasashen samar da gangar man fetur miliyan 1.84 a kowane rana, da kuma musayar kuɗi ₦1,400 kan kowace Dala ɗaya a shekarar 2026.

Tsaro ya samu kaso mafi tsoka a kasafin

A bangaren rabon kuɗaɗen kasafin, tsaro da kare ƙasa ya samu mafi girman kaso na Naira tiriliyan 5.41, yayin da bangaren gina ababen more rayuwa ya samu Naira tiriliyan 3.56.

Sai kuma bangaren harkokin Ilimi da ya ya samu Naira tiriliyan 3.52, da kuma bangaren lafiya, wanda ya samu kason Naira tiriliyan 2.48.

An sanya wa kasafin kuɗin taken “Budget of Consolidation, Renewed Resilience and Shared Prosperity," watau kasafin kara karfafawa, juriya da ci gaban tattalin arziki na bai daya.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a zauren Majalisar Tarayya Hoto: @OfficialABAT
Source: Facebook

Wasu kalaman Tinubu a gaban Majalisa

Da yake jawabi ga ‘yan majalisa, Shugaba Tinubu ya jaddada cewa kasafin ba wai kawai jerin lambobin lissafi ba ne, bayanai ne na abubuwan da kasar za ta ba muhimmanci.

Kara karanta wannan

Gwamna Fubara ya fadi biliyoyin da ya tarar a asusun Rivers bayan cire dokar ta baci

Tinubu ya ce:

“Wannqn kasafin kuɗi bayani ne na abubuwan da ƙasa ta fi bai wa muhimmanci. Muna ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da daidaiton tsara dukiyar kasa, gaskiya wajen bashi, da kuma tabbatar da cewa duk kuɗin da ake kashewa yana da amfani ga al’umma.”

Tinubu ya sha alwashin samar da tsaro

A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya jaddada cewa dole ne a tabbatar da kafa 'yan sandan jihohi domin magance matsalar tsaro a Najeriya.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a yayin taron jam’iyyar APC karo na 14 da aka gudanar a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Ya ce kafa irin wannan tsari zai taimaka matuƙa wajen rage matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar, tare da bai wa jihohi damar ɗaukar nauyin kare al’ummominsu

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262