‘Ya Kamata a Rataye Shi’: Sanata Oshiomhole Ya Ji Daɗin Cire Farouk daga NMDPRA

‘Ya Kamata a Rataye Shi’: Sanata Oshiomhole Ya Ji Daɗin Cire Farouk daga NMDPRA

  • Sanata Adams Oshiomhole ya ce ya yi murnar murabus din shugabannin NMDPRA da NUPRC daga mukamansu
  • Oshiomhole ya ce ya ji dadi ne saboda haka ya zama dole domin ceto tattalin arzikin Najeriya daga rugujewa
  • Sanata David Jimkuta ya goyi bayan sanatan yayin tantance sababbin shugabannin hukumomin da Bola Tinubu ya tura

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Tsohon gwamnan jihar Edo, Sanata, Adams Oshiomhole, ya bayyana cewa ya yi murnar murabus din shugabannin NMDPRA da NUPRC.

Oshiomhole ya ce ficewar Injiniya Farouk Ahmed da Gbenga Komolafe daga mukamansu ya zama dole domin ceton tattalin arzikin Najeriya gaba daya.

Oshiomhole ya taso Farouk Ahmed a gaba kan almundahana
Tsogon shugaban hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed. Hoto: NNPC Limited.
Source: Twitter

Sanatan ya bayyana hakan ne yayin tantance mutanen da Shugaba Bola Tinubu ya nada shugabannin hukumar NUPRC da NMDPRA, cewar The Guardian.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zargin da Dangote ke yi kan Farouk

Kara karanta wannan

Bayan shiga APC, Gwamna Fubara ya bayyana shirinsa kan tazarcen Tinubu a 2027

Nadin ya biyo bayan murabus din Farouk Ahmed da Gbenga Komolafe, wadanda aka nada a 2021 karkashin dokar man fetur.

Sauyin ya biyo bayan rikici tsakanin Farouk Ahmed da shugaban rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, kan batun shigo da man fetur.

Dangote ya zargi NMDPRA da hana matatun mai na gida ci gaba ta hanyar bayar da lasisin shigo da man fetur daga waje.

Shugaba Tinubu ya mika sunan Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin shugaban NUPRC, da Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin shugaban NMDPRA.

Oshiomhole ya bukaci rataye Farouk Ahmed
Sanata Adams Oshiomhole daga jihar Edo. Hoto: The Nigerian Senate.
Source: Facebook

Sanata Oshiomhole ya dura kan Farouk Ahmed

A yayin tantancewar, Oshiomhole ya soki abin da ya kira manufofi marasa kan gado da tsohon shugaban ya aiwatar.

“Ina murna da aka cire su, har jiya ma da dare na yi murna, ya kamata a rataye shi, a magana ta a baya na ce idan ba a rataye shi ba, zai rataye Najeriya.
"Saboda duk wanda ke adawa da samar da ayyuka a Najeriya, ya zabi shigo da talauci Najeriya amma yake kai arzikinmu waje, bai kamata ya rayu ba."

Kara karanta wannan

NMDPRA: An maka Tinubu a gaban kotu game da rikicin Dangote da Farouk

Ya ce matsalar ba cancanta ba ce, illa dai manufofin da suka gurgunta masana’antu da kuma damar samar da ayyukan yi.

Sanatan Taraba ta Kudu, David Jimkuta, ya goyi bayan Oshiomhole yayin zaman Majalisar Dattawa, inda ya ce zai mara masa baya wajen tambayoyi ga sababbin shugabannin.

Yadda ake zargin Farouk da ruguza kasa

A cewarsa, Oshiomhole ya ce tsofaffin shugabannin sun fifita shigo da mai daga waje maimakon bunkasa matatun mai na cikin gida.

“Duk wanda baya son a samar da aiki a Najeriya, bai dace ya rike wannan bangare ba."

- In ji Oshiomhole.

Ya bukaci sababbin nadin su rika bin muradun kasa maimakon saukin kasuwanci ko ribar wasu ‘yan tsiraru, cewar Premium Times.

NMDPRA: An maka Tinubu a kotu

Mun ba ku labarin cewa wata kungiya ta shigar da kara a kotu kan zargin rashin gaskiya da ake yi wa tsohon Shugaban hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed.

Karar ta biyo bayan zargin da Aliko Dangote na cewa Farouk Ahmed na aikata almundahana da cin mutuncin kujerarsa.

Kara karanta wannan

NLC: Ajaero ya fadi sabon alkawarin da Tinubu ya dauka game da rashin tsaro

Kungiyar na neman a yi bincike, a dakatar, tare da gurfanar da tsohon Shugaban NMDPRA a gaban kotu domin gaskiya ta yi halinta.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.