Tinubu Ya Cire Sunan Ramat, Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar NERC

Tinubu Ya Cire Sunan Ramat, Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar NERC

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake nada sabon kwamitin hukumar kula da wutar lantarki ta Najeria, NERC
  • Hakan ya biyo bayan Majalisar Dattawa ta amince da mambobinsa domin karfafa bangaren wutar lantarki a kasar
  • Tinubu ya bukaci kwamitin NERC ya kara zurfafa gyaran bangaren wuta bisa dokar wuta ta shekarar 2023

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake kafa kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya, NERC.

Tinubu ya dauki wannan mataki ne bayan tantancewar da aka yi musu daga Majalisar Dattawa domin ci gaba da kawo sauyi a bangaren wuta.

Tinubu ya nada kwamitin gudanarwa na hukumar NERC
Shugaba Bola Tinubu yana sa hannu a wasu takardu. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

Hakan na cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar a shafin X.

Kara karanta wannan

Maganganun Tinubu da na ministansa sun saba kan kudin da aka samu a 2025

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An yi zanga-zanga kan Ramat a Abuja

Hakan na zuwa bayan rasa sunan Abdullahi Ramat wanda ke rike da kujerar a baya kafin ba Olalekan Oseni a baya.

Lamarin ya jawo ta da jijiyoyin wuya a jihar Kano da ma wasu sassan Najeriya da aka yi zanga-zanga a Abuja.

Wasu masu zanga-zanga sun nuna damuwa da cewa sun gaji da jira game da tantance shi inda suka dira majalisar dattawa don nuna fushinsu kan jinkirin.

Masu zanga-zangar sun sanar da majalisar illar rashin tabbatar da Ramat a shugabancin hukumar NERC.

Tinubu ya cire sunan Ramat daga shugabancin hukumr NERC
Shugaba Bola Tinubu da Abdullahi Ramat. Hoto: Bayo Onanuga, Engr Abdullahi Garba Ramat.
Source: Facebook

Sabon shugaban kwamitin gudanarwa na NERC

Majalisar Dattawa ta amince da mambobin kwamitin ne a ranar 16 ga Disamba, 2025, kamar yadda dokar wutar lantarki ta tanadar ta shekarar 2023.

An nada Dr Mulisiu Olalekan Oseni, wanda ya fara aiki a NERC tun shekarar 2017 a matsayin shugaban kwamitin daga ranar 1 ga Disamba, 2025.

Kara karanta wannan

Yadda zanga zangar 'yan kwadago ke gudana a Kano, Sokoto, sauran jihohi

Nadin Oseni zai ci gaba har zuwa lokacin da zai kammala wa’adinsa na shekaru 10 a hukumar, bisa tanadin dokar wutar lantarki ta kasa.

Dr Yusuf Ali, wanda aka fara nada shi kwamishina a 2022, ya zama mataimakin shugaban kwamitin daga 1 ga Disamba, 2025.

Sauran mambobin kwamitin gudanawarwar NERC

Sauran mambobin kwamitin sun hada da Nathan Rogers Shatti, Dafe Akpeneye, Aisha Mahmud Kanti Bello, Dr Chidi Ike da Dr Fouad Animashaun.

Dr Fouad Animashaun kwararre ne a fannin attalin arzikin makamashi, kuma ya taba rike mukamin shugaban hukumar kula da wutar lantarki ta jihar Lagos.

Shugaba Tinubu ya bukaci kwamitin NERC ya kara zurfafa sauye-sauyen bangaren wutar lantarki, tare da bin dokar wuta ta shekarar 2023 dalla-dalla.

Yadda Ramat ya rasa kujerarsa a NERC

A baya, kun ji cewa shugaba Bola Tinubu ya nemi majalisar dattawa ta tabbatar da sababbin Shugabannin NERC, amma babu sunan Abdullahi Ramat daga jihar Kano.

A baya, Majalisar Dattawan ta ce Injiniya Ramat, ya gamu da cikas bayan rikice-rikicen siyasa da koke-koken jama’a a kansa, wanda ya sa dole aka dakata daga maganar tantancewar.

Kara karanta wannan

Majalisar wakilai ta shiga dambarwar Dangote da shugaban NMDPRA

Rahotanni sun nuna rikicin siyasar Kano ya taka rawa wajen hana tabbatar da shi, yayin da gwamnati ke duba Dr. Oseni a matsayin sabon shugaban hukumar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.