Ba a Gama Murnar Cin Zabe ba, Yan Ta'adda Sun Sace Mataimakin Ciyaman da Kansiloli 2

Ba a Gama Murnar Cin Zabe ba, Yan Ta'adda Sun Sace Mataimakin Ciyaman da Kansiloli 2

  • Mayakan Boko Haram/ISWAP sun yi garkuwa da zababben mataimakin shugaban karamar hukumar Biu, Alhaji Saidu a jihar Borno
  • 'Dan siyasar yana daya daga cikin wadanda suka samu nasara a zaben kananan hukumomin da aka gudanar a Borno ranar Asabar da ta wuce
  • 'Yan ta'addan sun kuma sace wasu kansiloli biyu da matafiya da dama a harin da suka kai ranar Laraba a kan titin Biu zuwa Maiduguri

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Borno, Nigeria - ’Yan ta’adda da ake kyautata zaton mayakan Boko Haram/ISWAP ne sun yi garkuwa da sabon mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Biu da kansiloli biyu a Jihar Borno

Kara karanta wannan

Sarki ya hada tawaga zuwa wajen Tinubu, sun goyi bayan tazarcensa a 2027

Rahotanni sun nuna cewa ’yan ta’adda sun sace mutanen ne kwanaki kadan bayan zaben kananan hukumomin Borno, wanda aka gudanar ranar Asabar, 13 ga watan Disamba, 2025.

Jihar Borno.
Taswirar jihar Borno da ke Arewacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Vanguard ta tattaro cewa wadanda 'yan ta'addan suka yi garkuwa da su sun hada da Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Biu, Alhaji Saidu, tare da kansiloli biyu da ke wakiltar mazabun Zarawuyaku da Miringa, a Jihar Borno.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda aka sace matafiya a Borno

An ce lamarin ya faru ne a yammacin ranar Laraba a tsakanin ƙauyen Kamuya da hanyar Buni Yadi, yayin da mutanen ke kan hanyarsu daga Biu zuwa Maiduguri, babban birnin jihar.

Haka kuma, wasu fasinjoji da ba a tantance su ba, waɗanda ke tafiya a cikin wata motar Hizbah daga garin Potiskum na Jihar Yobe zuwa Biu, suma sun fada hannun masu garkuwa da mutanen.

Wata majiya mai ƙarfi ta bayyana cewa ɗaya daga cikin kansilolin da aka sace shi ne tsohon mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Biu da ya gabata, cewar rahoton Daily Post.

'Dan siyasa ya roki jami'an tsaro

Wani babban ɗan siyasa a yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce:

Kara karanta wannan

Kakakin Majalisa na neman haddasa rigima a jam'iyyar APC kan tikitin zaben 2027

“Eh, sabon zaɓaɓɓen Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Biu, Alhaji Saidu, da kansiloli biyu masu wakiltar Zarawuyaku da Miringa, sun fada hannun ’yan Boko Haram/ISWAP a tsakanin Kamuya da hanyar Buni Yadi.
“An sace su ne tare da wasu fasinjoji da ke tafiya a motar Hizbah daga Potiskum zuwa Biu. Muna roƙon gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara zage damtse domin ceto su da sauran mutanen da ke hannun ’yan ta’adda lafiya.”
Gwamnq Babagana Zulum.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum Hoto: @ProfZulum
Source: Twitter

Titin Biu–Buratai–Kamuya–Buni–Damaturu mai tsawon kusan kilomita 120 ya shahara wajen zama hadari ga matafiya saboda yawan hare-haren yan ta'adda.

Sojoji sun yi kuskuren jefa bam a Borno

A wani rahoton, kun ji cewa jiragen yaki na Rundunar Sojojin Sama ta Najeriya (NAF) sun yi kuskuren jefa bama-bamai kan fararen hula a jihar Borno.

An kashe fararen hular ne a yayin wani hari da sojojin saman suka kai kan wuraren da ake zargin ’yan ta’adda ke amfani da su a jihar Borno a ranar Lahadi da ta gabata.

Rahotanni sun ce sojojin sun saki ruwan bama bamai kan masunta da direbobin motocin haya da suka taru a tsakanin Daban Masara a Kukawa da Badeiri a karamar hukumar Marte.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262