Shugaba Tinubu Ya Karbi Bakuncin Gwamnoni 3, Ya Gana da Su Daya bayan Daya

Shugaba Tinubu Ya Karbi Bakuncin Gwamnoni 3, Ya Gana da Su Daya bayan Daya

  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya karbi bakuncin gwamnonin jihohin Benuwai, Kaduna da Kuros Riba a fadarsa da ke Abuja
  • Rahoto ya nuna cewa gwamnonin sun isa fadar shugaban kasa a lokuta daban-daban kuma kowane ya gana da Bola Tinubu a sirrince
  • Wasu majiyoyi sun bayyana cewa gwamnonin sun tattauna kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da shugaban kasa, amma babu sanarwa a hukumance

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gwamnonin jihohi uku a Najeriya sun ziyarci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke birnin tarayya Abuja.

Gwamnonin da aka gani sun isa fadar shugaban kasa da yammacin jiya Juma'a sun hada da Gwamna Uba Sani na Kaduna, Gwamna Hyacinth Alia na Benuwai da Gwamna Bassey Otu na Kuros Riba.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu yayin wata ganawa a fadar shugaban kasa, Abuja Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Tinubu ya yi ganawar sirri da gwamnoni 3

Kara karanta wannan

Wasu manya a Kano sun ajiye Abba a gefe, sun ce Barau suke so a 2027

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa Shugaba Bola Tinubu ya gudanar da ganawar sirri daban-daban da gwamnonin jihohin Kaduna, Benuwau da Kuros Riba a fadar gwamnati da ke Abuja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar rahoton, Shugaba Tinubu ya gana da kowane gwamna shi kadai kuma a lokaci daban-daban, a jiya Juma'a, 12 ga watan Disamba, 2025.

Gwamnonin sun isa Fadar Shugaban Ƙasa a lokuta daban-daban, inda kowannen su ya shiga ganawa ta musamman da Shugaba Tinubu.

Wannan ganawa na zuwa ne yayin da ake fuskantar tabarbarewar tsaro a sassan kasar nan, kuma galibin jihohin da gwamnonin ke shugabanci na fama da kalubale na tsaro.

Ba a fitar da wani cikakken bayani a hukumance daga fadar shugaban ƙasa game da abin da gwamnonin suka tattauna da shugaban kasa ba.

Abubuwan da ake zaton sun tattauna

Sai dai majiyoyi da ke da masaniya kan ganawar sun ce an mayar da hankali ne kan matsalolin tsaro da sauran manyan batutuwan mulki da kalubale da ke addabar jihohin uku.

Daga cikin abubuwan da majiyoyin suka ce an tattaunawa akwai rikice-rikice tsakanin al’umma, ayyukan ’yan bindiga, da matsin tattalin arziki da ke ƙaruwa.

Kara karanta wannan

Bayan komawa APC, Gwamna Fubara ya yi wa Tinubu alkawari kan zaben 2027

Bayan kammala ganawar, gwamnonin ba su tsaya sun yi magana da ’yan jarida ba, sun dai yi gajeriyar gaisuwa kawai da manema labarai kafin su shiga motocinsu su bar fadar shugaban kasa.

Shugaba Tinubu da Uba Sani.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Aso Rock da Gwamna Uba Sani a gidan gwamnatin Kaduna Hoto: @OfficialABAT, Uba Sani
Source: Twitter

Har kawo yanzu da muke hada wannan rahoto, babu wata sanarwa daga fadar shugaban kasa ko daga bangaren gwamnonin Kaduna, Benuwai da Kuros Riba kan wannan ganawa da suka yi.

Bola Tinubu ya gana da gwamnonin APC 6

A wani rahoton, kun ji cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da gwamnonin jam'iyyar APC shida a fadar shugaban kasa da ke birnin tarayya Abuja a ranar Litinin.

Rahoton ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin bayan isarsu fadarsa, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a bayan fage.

An kuma rahoto cewa Mai Girma Tinubu da gwamnonin APC shida ba su shafe awa daya a wannan taron ba, kuma ba a yi wa 'yan jaridar fadar shugaban kasa wani bayani ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262