Jita Jita Ta Ƙare: Mataimakin Gwamna da Aka Garzaya da Shi Asibiti Ya Mutu Yanzu

Jita Jita Ta Ƙare: Mataimakin Gwamna da Aka Garzaya da Shi Asibiti Ya Mutu Yanzu

  • PDP ta kawo karshen jita-jitar da ake yadawa game da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo
  • A cikin wata sanarwa da ta fitar, jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar Sanata Ewhrudjakpo jim kadan bayan ya yanke jiki ya fadi a ofishinsa
  • Gwamnatin Bayelsa ba ta fitar da sanarwa ba tukuna, amma dai PDP ta miƙa ta’aziyya ga iyalai, gwamnati da jama’ar jihar baki daya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja – Jam’iyyar PDP ta tabbatar da rasuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Oboraw-Harievwo Ewhrudjakpo, a ranar Alhamis, 11 ga Disamba, 2025.

Legit Hausa ta rahoto cewa tun da sanyin safiyar Alhamis din ne aka fara samun tashin hankula kan lafiyar mataimakin gwamnan bayan rahotanni sun nuna cewa ya yanke jiki ya fadi a ofishinsa.

Kara karanta wannan

Sanata Ndume da Oshiomhole sun gwabza a majalisa kan tantance Omokri

Jam'iyyar PDP ta tabbatar da rasuwar Sanata Lawrence, mataimakin gwamnan jihar Bayelsa
Mataimakin gwamnan Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo da ya rasu a ranar Alhamis, 11 ga Disamba, 2025. Hoto: Sen. Lawrence Ewhrudjakpo
Source: Facebook

PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamna

A cikin wata sanarwa da ta fitar da yammacin Alhamis a shafinta na X, PDP ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki (SAN), ta bakin sakataren yaɗa labarai na ƙasa, Ini Ememobong, ta bayyana cewa mutuwar ta girgiza jam'iyyar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai har yanzu gwamnatin jihar Bayelsa ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da rasuwar mataimakin gwamnan ba.

A cikin sanarwar, PDP ta bayyana Sanata Ewhrudjakpo a matsayin ɗan jam’iyya mai aminci da rikon amana, tana mai cewa rasuwarsa ta jefa jam’iyyar, musamman reshen Bayelsa, cikin tashin hankali da baƙin ciki.

PDP ta yi addu’ar Allah ya jiƙansa ya kuma bai wa iyalansa, gwamnatin jihar Bayelsa da al’ummar jihar haƙurin jure wannan babban rashi.

Abin da PDP ta ce kan mutuwar Lawrence

Sanarwar PDP ta ce:

“Jam’iyyar PDP ta girgiza matuka da samun labarin mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Mai girma Sanata Lawrence Oborawharievwo Ewhrudjakpo. Wannan labari ya jefa mambobin NWC da daukacin jam’iyyar cikin baƙin ciki.”

Kara karanta wannan

Mataimakin gwamnan Bayelsa ya mutu? An gano gaskiyar halin da yake ciki a asibiti

Jam’iyyar ta bayyana cewa Ewhrudjakpo ya kasance ɗan siyasa nagari, mai tsayin daka ga gaskiya da akida, ba dan siyasar da ke canza ra’ayi saboda son kai ba.

PDP ta ce mataimakin gwamnan ya kasance “gwarzo a siyasa” wanda ya tsaya kan gaskiya har zuwa ƙarshen rayuwarsa.

Wanene mataimakin gwamnan Bayelsa?

Sanata Ewhrudjakpo ya kasance mataimakin gwamnan Bayelsa tun bayan nadewa a matsayin abokin takarar Gwamna Douye Diri a zaben gwamna na 2019, sannan an sake zaɓen su tare a 2023.

Ya rasu yana rike da wannan mukami.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com