'Dalilin da ya sa juyin mulki ba zai taɓa yiwuwa a Najeriya ba'

'Dalilin da ya sa juyin mulki ba zai taɓa yiwuwa a Najeriya ba'

  • Tsohon soja a Najeriya, Janar John Enenche mai ritaya ya yi magana kan yiwuwar juyin mulki a kasar duba da abin da ke faruwa
  • Enenche ya bayyana cewa juyin mulki yanzu kusan ya zama ba zai yiwu ba a Najeriya saboda sabuwar fahimtar dimokuradiyya cikin sojoji
  • Ya ce horo da kwarewar da aka ba jami’an soja tun bayan mulkin Ibrahim Babangida sun canja tunaninsu

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Tsohon Daraktan Bayanai na Sojoji, Janar John Enenche mai rataya ya bayyana yiwuwar samun juyin mulki a Najeriya.

Enenche ya ce juyin mulki yanzu kusan ya zama “ba zai yiwu ba” saboda tsarin tunani a rundunar soji wnada zai yi wahala a yi juyin mulki.

Tsohon Janar ya magantu kan yiwuwar juyin mulki a Najeriya
Tsohon Janar a Najeriya, John Enenche. Hoto: HQ Nigeria Army.
Source: Facebook

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin hira a Sunday Politics a Channels TV, ya ce jita-jitar juyin mulki ba ta dame shi sosai ba. Enenche ya jaddada cewa sabon tsari da aka dora jami’an sojoji baya goyon bayan kifar da gwamnati.

Kara karanta wannan

Shekaru 15 ana abu 1: Olusegun Obasanjo ya fadi hanyar kawar da Boko Haram

Ya ce horo da koyarwar da rundunar soji ta samu shekaru 30 da suka gabata sun bayyana cewa gwamnatin soja bata dace ba kuma ba ta amfanar ma’aikata.

Ya tunatar da cewa rundunar soji ta sha wahala a zamanin mulkin soja, inda kayayyaki, jin dadi da ci gaban cibiyoyi suka tsaya gaba daya a wancan lokacin.

Enenche ya ce irin wadannan abubuwa sun canja tunanin jami’an soja na yau, suna ganin shiga siyasa ba abu ne mai amfani ga rundunar ko kasa ba.

Ya nuna cewa juyin mulki ya fi yawa a wasu kasashen Yammacin Afirka saboda rashin zurfin dimokuradiyya da tarihi mai cike da matsalolin siyasa da tasirin mulkin mallaka.

Tsohon janar din ya ce mafi yawan kasashen da ke fuskantar juyin mulki Francophone ne, inda ake ganin rashin gamsuwa da tasirin kasashen Turai tun bayan samun ‘yanci.

Ya yi misali da Mali wadda kusan ta katse hulda da Faransa, yana cewa irin wannan yanayi ya nuna dalilin da yasa Anglophone basu cika shiga juyin mulki ba.

Duk da cewa ba ya ganin juyin mulki zai yiwu a Najeriya, ya gargadi cewa rikici a makwabtan kasashe zai iya shafar tsaro, tattalin arziki da harkokin kasuwanci.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta dauki matakai 3 bayan sojoji sun yi yunkurin juyin mulki a Benin

Ya ce barazanar rikicewa a Benin ko sauran kasashe na iya jawo durkushewar kasuwanci da yawaitar hijira zuwa Najeriya kamar yadda aka gani a Libya.

Duk da cewa ba ya ganin juyin mulki zai yiwu a Najeriya, ya gargadi cewa rikici a makwabtan kasashe zai iya shafar tsaro, tattalin arziki da harkokin kasuwanci.

Ya ce barazanar rikicewa a Benin ko sauran kasashe na iya jawo durkushewar kasuwanci da yawaitar hijira zuwa Najeriya kamar yadda aka gani a Libya.

Tinubu zai tura sojoji Jamhuriyar Benin

Kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya samu amincewar Majalisar Dattawa domin daukar mataki mai tsauri a Jamhuriyar Benin.

Hakan ya biyo bayan yunkurin juyin mulki da aka yi a kasar wanda bai yi nasara ba a ranar Lahadi 7 ga watan Disambar 2025.

Tinubu ya ce Benin ta nemi tallafin jiragen yaki na Najeriya, domin dakile barazanar yan tawaye da ke neman rusa dimokuraɗiyya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.