Tsohon Hadimin Tinubu Ya Kalubalanci Shugaban Kasa game da Takarar 2027
- Tsohon mashawarcin Kashim Shettima kan harkokin tsaro, Hakeem Baba-Ahmed ya sake bayar da shawara ga Bola Tinubu
- Ya ce bai kamata Shugaban Kasa ya rika tunanin sake tsayawa takara ba matukar da gaske ya ke kaunar ci gaban kasar nan
- Dr. Hakeem Baba Ahmed ya bayyana cewa shekaru biyun da rabi da Tinubu ya yi a mulki sun fito da gazawarsa baro-baro
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
FCT Abuja – Tsohon ma ba Mataimakin Shugaban Kasa shawara kan harkokin siyasa, Hakeem Baba Ahmed ya ba Bola Tinubu shawara game da zaben 2027.
Dr. Hakeem Baba-Ahmed, ya bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sake nazari kan ci gaba da rike kujerarsa bayan shekarar 2027.

Source: Twitter
Jaridar Leadership ta wallafa cewa tsohon hadimin Shugaban Kasa ya kara da cewa saukar Tinubu daga mulkin Najeriya zai fi zama alheri da rike kujerar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hakeem Baba Ahmed ya shawarci Bola Tinubu
Daily Post ta wallafa cewa Baba-Ahmed ya ce shekaru biyu da rabi da Tinubu ya shafe a mulki sun nuna cewa ba zai iya ba.
Ya bayyana cewa akwai babban gibi tsakanin abin da gwamnati ke cewa tana yi da abin da ‘yan Najeriya ke fuskanta.
A cewarsa, talauci da wahala sun karu, al’umma na cikin halin tsadar rayuwa, kuma matsalolin tsaro sun ta’azzara fiye da yadda aka bar su a mulkin baya.
Ya ce:
“Abin da yake cewa yana yi ya da bambanci da abin da mutane ke gani a yau.”
'Ana wahala a mulkin Tinubu' - Hakeem Baba-Ahmed
Ya kara da cewa tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Najeriya cikin mawuyacin halin tsaro, amma a yanzu ma babu ci gaba.
Hakeem Baba Ahmed ya ce:
“Tinubu bai inganta komai ba; maimakon haka al’amura sun kara tabarbarewa.”
“Idan Shugaba Tinubu na son ganin Najeriya ta tsira, ina ganin lokaci ya yi da zai yi murabus.”

Source: Facebook
Ya ce duk da cewa mulkin dimokuradiyya na ba da damar shugaban kasa ya tsaya takara har sau biyu, al’ummar Najeriya su fara tunanin samun sabon shugaba a shekarar 2027.
Tsohon mai ba da shawarar ya kuma jaddada cewa ci gaban Najeriya ya fi muhimmanci fiye da a bar gwamnati a hannun wanda ba ya kawo sauyi.
A cewarsa, Najeriya tana bukatar shugaba mai kuzari, hangen nesa da dabarun warware matsalolin tsaro, tattalin arziki da jin dadin jama’a.
Hakeem Baba Ahmed ya tabo Atiku
A wani labarin, mun wallafa cewa Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana mahangarsa kan siyasar Najeriya gabanin zaben 2027 da burin neman takarar Atiku Abubakar.
Tsohon hadimin Shugaban Kasan ya shawarci dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, da ya sake tunani kan kudirinsa na komawa takara.

Kara karanta wannan
"Akwai abin da ba a karya da shi": Rarara ya fadi dalilin aikin alheri a kauyensu
Ya ce lokaci ya yi da Atiku, wanda ya taba rike mukamin mataimakin shugaban kasa na tsawon shekaru takwas a mulkin Olusegun Obasanjo, ya daina neman shugabanci.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

