Sojoji Sun Toshe Kofofin Tsira ga 'Yan Bindiga a Sokoto, an Hallaka Tsageru
- Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar dakile wani mugun nufi na 'yan bindiga a jihar Sokoto da ke yankin Arewa maso Yamma
- Sojojin sun kubutar da 'yan kasuwan da 'yan bindiga suka yi wa kwanton bauna lokacin da suke kan hanyar zuwa neman na abinci
- Jami'an tsaron sun yi raga-raga da 'yan bindigan inda suka hallaka wasu daga cikinsu tare da kwato babura da bindigogi a hannunsu
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Sokoto - Dakarun sojoji sun kashe wasu da ake zargin ’yan bindiga ne yayin wani artabu a jihar Sokoto.
Sojoji sun hallaka 'yan bindigan ne bayan kai dauki don ceto ’yan kasuwa da aka yi wa kwanton-bauna a kan hanyar Tarah–Karawa da ke karamar hukumar Sabon Birni a jihar Sokoto.

Source: Twitter
Jaridar Daily Trust ta ce 'yan kasuwar na cikin tafiya daga kauyen Tarah zuwa kasuwar mako ta Sabon Birni ne maharan suka tare su a Kwanan Akimbo da misalin karfe 8:00 na safe.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sojoji sun ragargaji 'yan bindiga a Sokoto
Wasu mazauna yankin sun ce sojojin da ke sansaninsu a garin Kurawa sun ji harbe-harbe, inda suka yi gaggawar isa wurin, lamarin da ya jawo musayar wuta wadda ta ɗauki kusan awa guda.
Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa sun kirga gawarwakin 'yan bindigan da sojojin suka kashe.
“Sojoji sun yi artabu da su sosai. Daga baya ’yan bindigar suka ja da baya suka gudu zuwa maboyarsu a bayan rafi."
"Mun kirga gawarwakin 'yan bindiga tara a nan cikin yankinmu, sannan an sake samun wasu huɗu a cikin daji da gefen rafin.”
“Sojoji sun kwashe makamai da babura da yawa daga wurin, suka tafi da su Kurawa.”
- Wata majiya
Ya kara da cewa mutane biyu ne suka ji rauni daga bangaren fararen hula kuma suna karɓar magani a asibiti, amma an ceto dukkan ’yan kasuwar cikin koshin lafiya ba tare da wani lahani ba.
Hakazalika ya bayyana cewa babu wani soja da ya ji rauni a bangaren jami'amn tsaron.
An gano gawarwakin 'yan bindiga
Da yake tabbatar da lamarin, dan majalisar jiha mai wakiltar Sabon Birni, Hon. Aminu Boza, ya ce an gano gawarwaki akalla tara da ake zargin na maharan ne, kuma ana ci gaba da bincike a yankin.

Source: Original
“An samu makamai da babura da yawa daga hannunsu. Ina fatan sojojinmu za su ci gaba da wannan kokarin."
- Aminu Boza
Wannan hari dai ya faru ne kwana ɗaya bayan wasu ’yan bindiga sun kai hari a kauyukan Gatawa da Shalla a Sabon Birni da Isa, inda suka kashe mutane guda bakwai tare da yin garkuwa da mata da dama.
'Yan bindiga sun kai hari a Sokoto
A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a wani kauyen jihar Sokoto.
Yan bindigan sun kashe mutum biyu tare da yin garkuwa da mutane 15, ciki har da wasu mata huɗu masu shayarwa da jariransu a harin da suka kai a kauyen Kurawa.

Kara karanta wannan
Ba wasa: Matakin da Gwamna Abba zai dauka don dakile hare haren 'yan bindiga a Kano
Dan majalisar da ke wakiltar yankin, Hon. Sa’idu Ibrahim, ya ce mutum 15 ne maharan suka tafi da su yayin harin da suka kawo.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng

