Gwamnoni 6 Sun Dura Fadar Aso Rock, Sun Shiga Ganawa da Shugaba Tinubu

Gwamnoni 6 Sun Dura Fadar Aso Rock, Sun Shiga Ganawa da Shugaba Tinubu

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da gwamnonin jam'iyyar APC shida a fadar shugaban kasa da ke birnin tarayya Abuja a ranar Litinin
  • Gwamnonin da suka halarci wannan ganawa sun hada da Ahmad Aliyu (Sokoto), Lucky Aiyedatiwa (Ondo) da Umar Namadi (Jigawa)
  • Jihohin Kebbi, Sokoto da Kogi, da gwamnoninsu suka sanya labule da Tinubu sun fuskanci hare-haren 'yan bindiga a 'yan watannin nan

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Rahotanni da ke shigo mana na nuni da cewa wasu gwamnoni shida na jam'iyyar APC sun dura fadar shugaban kasa da ke babban birnin tarayya Abuja.

Rahoton ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin bayan isarsu fadarsa, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a bayan fage.

Gwamnonin APC shida sun gana da Tinubu a fadar shugaban kasa Abuja.
Shugaba Bola Tinubu ya saka labule da gwamnonin APC 6 a fadar shugaban kasa Abuja. Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Gwamnonin sun shiga ofishin shugaban kasa da misalin karfe 4:00 na yammacin yau Litinin, 8 ga watan Disamba, 2025 kamar yadda jaridar Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Mutane sun yi mamaki da Uwargidan Tinubu ta 'kunyata' gwamna a bainar jama'a

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An kuma rahoto cewa Tinubu da gwamnonin shida ba su shafe awa daya a wannan taron ba, kuma ba a yi wa 'yan jaridar fadar shugaban kasa wani bayani ba.

Har zuwa lokacin fitar da wannan rahoto, Legit Hausa ba ta samu bayani game da makusin wannan taron ba.

Amma mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya fitar da sanarwa game da ganawar a shafinsa na X.

Bayo Onanuga ya ce:

"Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karbi bakuncin gwamnan Sokoto, Ahmad Aliyu, gwamnan Ondo, Lucky Aiyedatiwa, gwamnan Jigawa, Umar Namadi, gwamnan Kebbi, Dr. Nasir Idris, gwamnan Kogi, Ahmed Usman Ododo da gwamnan Edo, Monday Okpebholo a fadar shugaban kasa."

Tinubu ya dauki matakai kan tsaro

Jaridar Punch ta rahoto cewa wannan taron na zuwa ne yayin da Najeriya ta fuskanci sababbin matsalolin tsaro, ciki har da sace daliban makarantu, masu ibada a Arewa maso Yamma da ta Tsakiya, wadanda aka ceto su daga baya.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya jingine banbancin siyasa, ya ba gwamna lambar yabo a Abuja

Jihohi da dama, kamar Kebbi, Sokoto da Kogi, da gwamnoninsu suka halarci zaman sun fuskanci hare-haren 'yan bindiga da masu garkuwa da mutane a 'yan watannin nan.

A ranar 26 ga Nuwamba, 2026 Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a wani mataki na dakile yawaitar hare-haren 'yan ta'adda a sassan kasar.

Sannan Tinubu ya ba sojoji, 'yan sanda da hukumomin leken asiri umarnin kara yawan wadanda za a dauka aiki da tura dakaru da yawa a jihohin da ke fuskantar hare-hare.

Gwamnoni sun yi gum bayan ganawa da Tinubu

Ya kuma bukaci jami'an tsaro da su ba da fifiko a tsaron makarantu, gonaki da wuraren ibada, yayin da gwamnonin jihohi suka dauki nasu matakan kariya.

Hakazalika, an samu sauyin ministan tsaro a makon jiya, da kuma neman taimako daga kasashen waje don yaki da ta'addanci a Najeriya.

Ko da 'yan jaridar da ke dauko rahoto a fadar shugaban kasa suka tare su bayan kammala wannan zama, gwamnonin ba su ce uffan a kai ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com