An Samu Matsala: Jirgin Saman Sojojin Najeriya Ya Yi Hatsari a Jihar Neja

An Samu Matsala: Jirgin Saman Sojojin Najeriya Ya Yi Hatsari a Jihar Neja

  • Wani jirgin sama na rundunar sojojin Najeriya ya gamu da hatsari a kusa da Karabonde, cikin Karamar Hukumar Borgu ta jihar Neja
  • Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa matukan jirgin sun samu nasarar fita lafiya tun kafin jirgin ya kife da yammacin yau Asabar
  • Rundunar sojojin sama ba ta ce komai ba kawo yammacin na yau amma an fara yada bidiyoyin yadda jirgin ya kama da wuta bayan hatsarin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Niger, Nigeria - Rahotanni daga jihar Neja da ke Arewa ta Tsakiya a Najeriya sun nuna cewa wani jirgin rundunar sojojin sama (NAF) ya gamu da hatsari.

Bayanai sun nuna cewa jirgin yakin sojojin ya fado kasa tare da kamawa da wuta a kusa da Karabonde, cikin Karamar Hukumar Borgu ta jihar Neja.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya 'wawure' Naira biliyan 16.5 na gyaran gadar Arewa? Gaskiya ta fito

Jihar Neja.
Taswirar jihar Neja da ke Arewa ta Tsakiya a Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Rahoton jaridar Punch ya nuna cewa matukan jirgin biyu sun tsira bayan sun yi amfani da rigar sauka ta gaggawa kafin jirgin ya fadi kasa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wani gidan talabijin na yanar gizo da ke jihar Neja, Lapai TV, ya wallafa faifan bidiyon wurin da jirgin ya yi hatsari a shafinsa na Facebook da yammacin yau Asabar.

Yadda jirgin sojoji ya fado a Neja

Wani ganau ya shaida wa jaridar ta hanyar sakon murya cewa matukan jirgin sun samu nasarar fita lafiya kafin jirgin ya yi ƙasa da ya fadi da karfi.

Ya ce:

“Muna tsammanin jirgin ya taso ne daga sansanin sojin sama na Kainji. Bayan aukuwar lamarin mun fahimci jami'an sojojin sama sun fara tattaki zuwa wurin hatsarin.”

A wata tattaunawa ta waya, wani mazaunin yankin mai suna Lukman Sulaiman ya ce hatsarin jirgin sojojin Najeriya ya faru ne misalin karfe 4:10 na yamma.

Kara karanta wannan

Wani bam ya tarwatse da mutane a Banki, an samu asarar rayuka a jihar Borno

"Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:10 na yamma. Jirgin ya fado ne kusa da gari amma Allah Ya kiyaye, matukan jirgin sun yi nasarar ficewa lafiya," in ji shi.

Halin da mutane suka shiga bayan hatsarin

Da aka tambaye shi ko matukan jirgin ba su ji rauni ba, ya ce, "Eh, mun ji karar fadowar jirgi mai kara da karfi, mun tsorata, amma daga ƙarshe muka fara tafiya zuwa wurin da abin ya faru."

Ya kara da cewa jama’a sun firgita da karar fashewar da suka ji kafin su fara mamaye wajen da lamarin ya faru.

Jirgin sojoji.
Jirgin rundunar sojin saman Najeriya yayin da ya lula sararin samaniya Hoto: @AirForceHQ
Source: Twitter

Bidiyoyi biyu da ake yadawa sun nuna jirgin Alpha Jet ɗin yana ƙonewa a cikin daji bayan ya fadi.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton, rundunar sojin saman Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa game da hatsarin ba.

Jiragen sojoji sun yi luguden wuta a Neja

A wani rahoton, kun ji cewa jiragen sojoji sun samu nasarar hallaka daya daga cikin manyan jagororin 'yan bindiga da suka addabi al'umma a jihar Neja.

Luguden wutan jiargen sojojin Najeriya ya hallaka Babangida, ɗaya daga cikin sanannun kwamandojin ’yan bindiga a karamar hukumar Shiroro.

Kara karanta wannan

Albishir da ministan tsaro ya fara yi ga 'yan Najeriya bayan shiga ofis a Abuja

An ce mutuwar Babangida ta raunana dabar Dogo Gide, wanda ya shahara wajen kai hare-hare masu tsanani a sassan Jihar Neja da makwabtan jihohi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262