Sufurin Jiragen Sama: Gwamnatin Tinubu Za Ta Karrama Dan Kano da Wasu Mutane 40

Sufurin Jiragen Sama: Gwamnatin Tinubu Za Ta Karrama Dan Kano da Wasu Mutane 40

  • Najeriya ta shirya taron murnar cika shekaru 100 da fara sufurin jiragen sama tun bayan saukar jirgi na farko Kano a 1925
  • Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya bayyana cewa bikin na musamman zai karrama gwaraza 41 a fannin sufurinjirage
  • Legit Hausa ta tattaro sunayen wadanda za a karrama, ciki har da mai kamfanin Kabo Air, watau Marigayi Muhammadu Dan Kabo

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - A ranar Litinin, 1 ga Disamba, 2025, Najeriya za ta gudanar da babban taro na kasa domin bikin cika shekaru 100 da fara sufurin jiragen sama a ƙasar.

Wannan bayani ya fito ne daga wata sanarwa da mai ba Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, shawara kan harkokin yada labarai, Tunde Moshood, ya fitar a Abuja.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: 'Yan bindiga sun sace mai martaba sarki a jihar Kwara

Gwanmnati za ta gudanar da taron murnar cikar Najeriya shekaru 100 da fara sufurin jiragen sama.
Hotunan mutane 41 da gwamnati za ta karrama ciki har da mai kamfanin Kabo Air. Hoto: @northern_trends, @fkeyamo
Source: Twitter

Bikin tunawa da saukar jirgin farko a Kano

Bikin zai gudana da misalin ƙarfe 10:00 na safe a African Hall da ke cikin babban dakin taron Bola Ahmed Tinubu, Abuja, in ji rahoton Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce za a yi duba kan tarihin samun ci gaban sufurin jiragen sama tun bayan zuwan jirgi na farko da ya sauka a Kano a 1925.

Haka kuma, bikin zai zama dandalin haɗuwa tsakanin kamfanonin jirage, hukumomin sufurin sama, masu kula da filayen jirage, kamfanonin kayan aiki, da kwararru daga bangarori daban-daban.

Akwai shirin gabatar da jawaba na musamman, haska fina-finan tarihi, da kuma gabatar da ayyukan da suka danganci ci gaban fannin sufuri.

Gwamnati za ta karrama Dan Kabo da wasu 40

Daya daga cikin manyan abubuwan da za su dauki hankali a bikin shi ne karrama manyan jarumai 41 da suka taka gagarumar rawa wajen bunkasa bangaren jiragen sama.

Kara karanta wannan

Yadda jikin Shehu Dahiru Bauchi ya yi tsanani, aka tafi da shi asibiti ya rasu

Festus Keyamo ya bayyana su a matsayin “gwarazan da hangen nesansu da sadaukarwarsu ta gina tushen cigaban jiragen sama a Najeriya.”

Sunayen sun haɗa da matuka jirage, injiniyoyi, kwararrun masu kula da zirga-zirgar jirage, shugabanni da masu kafa kamfanoni, kamar marigayi Alhaji Muhammad Adamu Dan Kabo na jihar Kano.

Sunayen mutane 41 da za a karrama

An fitar da sunayen mutane 41 da za a karrama, don tunawa da gudunmawarsu a sufurin jiragen saman Najeriya.
Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo a wani taro a Abuja. Hoto: @fkeyamo
Source: Facebook

Duba cikakkun sunayen a kasa, kamar yadda Minista Keyamo ya wallafa hotunansu a shafinsa na Facebook:

  1. Capt. Robert Hayes
  2. Capt. Prex Porbeni
  3. Mrs. Folashade Odutola
  4. Dr. Taiwo Afolabi OON
  5. Capt. Fola Adeola
  6. Dr. Seindemi Fadeni
  7. Capt. Chinyere Kalu
  8. Chief Wale Babalakin
  9. Harold Demuren
  10. Akin Olateru
  11. Capt. Ado Sanusi
  12. Mr. George Urensi
  13. Mrs. Deola Yesufu
  14. Engr. Babatunde Obadofin
  15. Dr. Ayo Obilana
  16. Pa Odeleye AC
  17. Capt. Toju Ogisi
  18. Pa Abel Kalu Ukonu
  19. Capt. Felix Iheanacho
  20. Capt. Peter Adenihun
  21. Capt. Jonathan Ibrahim
  22. Chief Gabriel Osawaru Igbinedion
  23. Sir Joseph Arumemi
  24. Olumuyiwa Bernard Aliu
  25. Capt. Dele Ore
  26. Alhaji Dan Kabo
  27. Capt. Wale Makinde
  28. Capt. Ibrahim Mshelia
  29. Capt. Dapo Olumide
  30. Ms. Bimbo Sosina
  31. Chief Allen Onyema
  32. Capt. Benoni Briggs
  33. Mrs. Deola Omikunle
  34. Dr. Thomas Ogungbangbe
  35. Capt. Edward Boyo
  36. Dr. Gbenga Olowo
  37. Elder Dr. Soji Amusan
  38. Engr. Awogbami Clement
  39. Sen. Musa Adede
  40. Georg Eder MBA
  41. Chief Mbazulike Amaechi

Kara karanta wannan

An kashe mutum 2 da ƴan bindiga suka je sace dalibai a Kogi? Gwamnati ta yi martani

Kayamo ya fadi dalilin Tinubu na ba shi minista

A wani labarin, mun ruwaito cewa, ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya rubuta budaddiyar wasika ga shugaban Amurka, Donald Trump.

Keyamo ya rubuta wasika inda ya ce Najeriya ba kasa ba ce da gwamnati ke zaluntar Kiristoci, kuma shi Kirista ne mai tsayin daka a cikin kasar.

Keyamo ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ya nada shi ne minista ne saboda kyakkyawar dabi'a, kishin kasa da tushensa a matsayin Kirista.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com