A Karon Farko cikin Shekaru 14, An Zabi Najeriya a Majalisar IMO Ta Duniya

A Karon Farko cikin Shekaru 14, An Zabi Najeriya a Majalisar IMO Ta Duniya

  • An zabi Najeriya ta shiga cikin rukunin C na Majalisar harkokin sufurin teku ta duniya watau IMO na shekarun 2026–2027
  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ce wannan nasara tana nuna yadda duniya ke amincewa da tasirin Najeriya a harkar sufurin teku
  • Najeriya ta bayyana cewa za ta yi aiki tare da ƙasashen duniya wajen kare teku da inganta tsaro da sufurin ruwa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Bayan shekaru 14 da rasa kujerarta, Najeriya ta koma Majalisar Kula da Harkokin Teku ta Duniya watau IMO.

Fadar shugaban kasa ta tabbatar da cewa an zabi Najeriya a Majalisar International Maritime Organisation (IMO) bayan tsawon lokaci da rasa wannan gurbi.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya da ke Abuja Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, 29 ga watan Nuwamba, 2025, kamar yadda Channels tv ta kawo labarin.

Kara karanta wannan

Jonathan ya gana da Tinubu, ya fada masa abin da ya faru da shi a Guinea Bissau

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana cewa an zabi Najeriya ne a rukunin C, inda za ta shafe wa'adin shekaru biyu daga 2026 zuwa 2027 a Majalisar DMO.

Onanuga ya ce Najeriya ta samu nasarar komawa IMO ne a zaben da aka gudanar a taron majalisar da aka yi a birnin Landan na Birtaniya a ranar Juma’a, 28 ga Nuwamba, 2025.

Shugaba Tinubu ya ji dadin nasarar Najeriya

Shugaba Bola Tinubu ya yi farin ciki da wannan ci gaba, yana mai bayyana nasaran a matsayin shaida ta irin tasirin Najeriya a harkokin tekun duniya,

Ya ce zaben da aka yi wa Najeriya ya nuna irin rawar da take takawa wajen tsare-tsare na zirga-zirgar jiragen ruwa a duniya.

Shugaban ya ce nasarar ta nuna yadda ƙasashen duniya suka aminta da tsarin tsaron tekun Najeriya, kare muhalli, bin doka sau da kafa da ingantaccen tsarin gudanar da harkokin ruwa.

Tinubu ya yabi Oyetola da NIMASA

Kara karanta wannan

Majalisa ta tsoma baki da Jonathan ya makale a kasar da sojoji suka yi juyin mulki

Shugaban Tinubu ya yaba da kokarin Ministan Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Dr. Adegboyega Oyetola, ma’aikatan ma’aikatarsa, hukumar NIMASA da tawagar diflomasiyyar Najeriya,

Tinubu ya ce wadannan sun cancanci yabo saboda jajircewa da dabarun da suka yi wajen tabbatar da nasarar Najeriya a zaben, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Ya ce sabon kudirin IMO ya yi daidai da manufofin gwamnatinsa na bude damar tattalin arzikin ruwa, habaka cibiyoyin ruwa da karfafa yaki da fashin teku.

Gbenga Oyetola.
Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Gbenga Oyetola Hoto: Gbenga Oyetola
Source: Twitter

Tinubu ya tabbatar wa kasashen duniya cewa Najeriya za ta inganta tsaro a teku, taimaka wajen kare muhalli, da gina ingantaccen tsarin jigilar kayayyaki ta jiragen ruwa,

Ya gode wa dukkan kasashen da suka mara wa Najeriya baya, yana mai cewa ƙasar za ta:

“Cika amanar da aka dora mata ta hanyar bayar da jagoranci nagari da himma wajen ci gaban harkokin sufuri da tsaron teku a duniya.”

Tinubu ya nada jakadun Najeriya 3

A wani rahoton, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya aikawa majalisar dattawa da sunayen mutane uku da yake son ya nada jakadu domin tantancewa da tabbatarwa

Kara karanta wannan

'Maganganun Tinubu ne suka jawo': Ministan Buhari kan karuwar rashin tsaro

Shugaba kasar ya ce an yi waɗannan naɗe-naɗen ne bisa tanadin sashe na 171 (1), (2)(c) da (4) na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da aka yi wa garambawul.

Ya roki majalisar dattawa da ta duba kuma ta tabbatar da waɗannan naɗe-naɗe cikin gaggawa, inda aka mika sunayen ga kwamitin harkokin kasashen waje na majalisar dattawa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262