Majalisa Ta Tsoma Baki da Jonathan Ya Makale a Kasar da Sojoji Suka Yi Juyin Mulki

Majalisa Ta Tsoma Baki da Jonathan Ya Makale a Kasar da Sojoji Suka Yi Juyin Mulki

  • Majalisar Wakilai ta bukaci gwamnatin Najeriya ta fara bin matakan diflomasiyya domin dawo da Goodluck Jonathan gida
  • Jonathan da sauran masu sa ido kan zaɓe sun makale a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a ranar Laraba da ta shige
  • Sojoji sun karɓi iko, sun dakatar da zaɓe, sun rufe iyakoki tare da kafa dokar hana fita da daddare a fadin kasar Guinea-Bissau

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - A jiya Laraba ne rundunar sojojin Guinea-Bissau ta tabbatar da karbe mulki tare da tsare shugaban kasa nan take.

Wannan juyin mulki da ya auku ya rutsa da tsohon shugaban Najeriya, Dr. Goodluck Jonathan, wanda ya je sanya ido kan zaben shugaban kasa da 'yan majalisu a Guinea-Bissau.

Shugaba Jonathan.
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan Hoto: Dr. Goodluck Jonathan
Source: UGC

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Majalisar Wakilai ta shiga lamarin domin tabbatar da Jonathan ya dawo gida Najeriya cikin koshin lafiya.

Kara karanta wannan

Abin da gwamnatin Tinubu ta ce kan juyin mulki a Guinea Bissau, ta yi gargadi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majalisa ta bukaci a dawo da Jonathan

Majalisar ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta gaggauta amfani da diplomasiyya da duk wasu matakai domin tabbatar da dawo da tsohon Shugaba Jonathan daga Guinea-Bissau.

Wannan matakin ya biyo bayan amincewa da wani kudirin gaggawa da shugaban masu rinjaye, Farfesa Julius Ihonvbere, ya gabatar a zaman yau Alhamis.

Ihonvbere ya shaida wa Majalisar cewa Jonathan, wanda ya je Guinea-Bissau domin sa ido kan zaɓe, ya makale bayan sojoji sun karɓi iko.

Rahotanni sun nuna cewa tsohon shugaban ƙasar ya makale tare da sauran masu sa ido na ƙasashen waje, bayan Sojoji sun karɓi iko da yammacin Laraba.

Wane hali Jonathan ke ciki a kasar?

"A halin yanzu, yana Guinea-Bissau saboda juyin mulkin," in ji Ihonvbere, yana mai jaddada cewa duk da cewa Majalisa ba ta tattauna kan juyin mulkin ba, tsaron Jonathan "abu ne mai muhimmanci ga ƙasa."

Ya ƙara da cewa hukumomin gwamnati da abin ya shafa sun san da wannan ci gaba kuma sun riga sun ɗauki matakai don tabbatar da cewa Jonathan ya dawo lafiya.

Kara karanta wannan

Kaduna: Limamin addini ya mutu a hannun 'yan ta'adda kafin a biya kudin fansa

Shugaban marasa rinjaye, Hon Kingsley Chinda ya goyi bayan wannan kira, yana mai jaddada cancantar Jonathan a fannin dimokuradiyya da kuma huldar da ke tsakaninsa da duniya baki daya.

Dan majalisar ya kuma lura cewa dole ne a ceto sauran 'yan Najeriya da juyin mulki ya rutsa da su ba tare da an yi watsi da su ba.

Goodluck Jonathan.
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan da Majalisar Wakilan Tarayya Hoto: Goodluck Jonathan
Source: Facebook

Matakin da Majalisar wakilai ta dauka

Daga nan, majalisar wakilai ta kasa ta amince da kudirin ta hanyar kada kuri'ar murya, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta kara himma wajen kokarin diflomasiyya don sauwaka dawowar Jonathan da kuma fifita tsaron dukkan 'yan Najeriya da rikicin ya shafa.

Majalisa ta nemi a rage tsadar taki

A wani rahoton, kun ji cewa Majalisar Wakilai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta dauki mataki game da tsadar takin zamani da kayan noma a Najeriya.

Yayin zaman majalisa, Hon. Yusuf Galambi ya nuna damuwa game da tsadar takin zamani a kasuwa wanda ya ke jefa manoma cikin masifa da kuma asara mai tarin yawa.

Bayan tattake wuri, majalisar wakilai ta bukaci Gwamnatin Tarayya ta rage farashin takin zamani da sauran kayan noma.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262