Neja: Wasu Dalibai da Aka Sace Sun Yi Dabara, Sun Gudo daga Hannun 'Yan Bindiga

Neja: Wasu Dalibai da Aka Sace Sun Yi Dabara, Sun Gudo daga Hannun 'Yan Bindiga

  • Dalibai 50 da aka sace a makarantar St. Mary’s Papiri a jihar Neja sun samu nasarar kubutowa daga hannun 'yan bindiga
  • Kungiyar CAN ta bayyana cewa har yanzu dalibai 236 da wasu ma’aikata 12 da daliban sakandare 14 na hannun ’yan bindiga
  • An saki sunayen daliban 50 da suka gudo yayin da jami'an tsaro ke kara kaimi wajen ganin an ceto sauran wadanda aka sace

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Neja - An samu babban cigaba a Neja bayan da yara 50 daga makarantar St. Mary da ke Papiri, suka kubuta daga hannun ’yan bindiga.

Harin, wanda ya faru a daren Juma’a, ya rikita al’ummar karamar hukumar Agwara, inda maharan suka kutsa makarantar, suka yi harbe-harbe.

Dalibai 50 daga makarantar ST. Mary sun kubuto daga hannun 'yan bindiga a Neja.
Hoton allon sanarwa da ke kwatanta hanyar zuwa makarantar ST. Mary, inda aka sace dalibai a Neja. Hoto: GovBago/X
Source: UGC

Dalibai 50 sun gudo daga hannun 'yan bindiga

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa 'yan bindigar sun harbe wani mai gadi sannan suka yi awon gaba da daruruwan dalibai tare da malamai.

Kara karanta wannan

Ana neman daliban Kebbi, 'yan sanda sun ceto mata 25 da aka yi garkuwa da su

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahoton farko ya nuna cewa ma'aikata 12 da dalibai 215 aka sace amma bayan sake duba lamarin da kuma kirga dalibai, aka gano cewa har yanzu akwai wasu 88 da ba a san inda suke ba.

A cikin sabuwar sanarwar da aka fitar a ranar Lahadi ta hannun hadimin shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) na jihar, Daniel Atori, an tabbatar da cewa dalibai 50 sun tsere daga hannun maharan kuma sun koma gidajensu lafiya.

Sanarwar ta ce:

"Muna sanar da ku cewa a ranar Lahadi, 23 ga Nuwamba, 2025, mun samu rahoto mai faranta rai, cewa dalibai 50 sun kubuto daga hannun 'yan bindiga, kuma sun hadu da iyayensu."

Saura daliai 236 a hannun 'yan bindiga

Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna, wanda shi ne shugaban makarantar, ya bayyana cewa makarantar tana da tsarin kwana da jeka-ka-dawo a makarantar, kuma sashen firamare na da dalibai 430, daga cikinsu 377 'yan makarantar kwana ne, 53 kuma ’yan jeka-ka-dawo ne.

Kara karanta wannan

Matawalle ya yi bayani bayan gano wurin da aka boye 'daliban da aka sace a Kebbi

Ya ce har yanzu akwai dalibai 236 a hannun masu garkuwar, sannan akwai yara uku na masu aiki da aka kama, da kuma daliban sakandare 14.

Ma’aikata 12 na makarantar su ma suna tsare. Wannan ya nuna cewa daruruwan mutane – yara kanana, matasa da manya – har yanzu suna cikin hadari a dazuzzukan da ke tsakanin Niger, Kebbi da Sakkwato.

An ce har yanzu akwai fiye da dalibai 150 da ke hannun 'yan bindiga
Taswirar jihar Niger da ke Arewacin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Sunayen dalibai 50 da suka kubuto

Rabaran Yohanna ya roki al'umma da su ci gaba da addu'a domin kubutar sauran dalibai da ma'aikatan da aka sace.

Daliban da aka sace su ne:

1. Samson Bitrus

2. Emmanuel Francis

3. Amos Mathew

4. Timothy Peter

5. Ayuba Victor

6. Bulus Emmanuel

7. Bulus Samaila

8. Caleb Hosea

9. Catherine Emmanuel

10. Christopher Ezekiel

11. Dominic Daniel

12. Dominic Elisha

13. Elisha Harunna

14. Elisha Yakubu

15. Ezekiel Emmanuel

16. Ezekiel Joel

17. Ezekiel Pius

18. Ezra James

19. Friday Joel

20. Gloria Jeremiah

21. Godiya Mathew

Kara karanta wannan

An sake neman dalibai kusan 100 an rasa bayan hari a makarantar Neja

22. Iliya Philip

23. Ishaya David

24. Joseph Sunday

25. Julius Paul

26. Justina Adamu

27. Keziah Musa

28. Lawrence James

29. Lawrence Yohanna

30. Marcus Bulus

31. Mariam Joshua

32. Mathew Dauda

33. Micah Luka

34. Michael Jacob

35. Musa Timothy

36. Naomi Bulus

37. Nicodemus Ibrahim

38. Peter Jonathan

39. Pricillia Peter

40. Emmanuel Godwin

41. Samaila Dauda

42. Stephen Anthony

43. Sunday Shedrack

44. Veronica Iliya

45. Victoria Ishaku

46. Vincent Emmanuel

47. Wisdom Fabian

48. Yakubu Saminu

49. Yunusa Musa

50. Yusuf Sunday

Dalibai da malamai 277 ne aka sace a Neja

A wani labarin, mun ruwaito cewa, kungiyar CAN ta tattara adadin dalibai da malaman da 'yan bindiga suka sace a makarantar Katolika da ke Neja.

Wannan hari da yan bindiga suka kai makarantar da tsakar dare ya tada hankulan mutane daga sassa daban-daban na kasar nan.

Kara karanta wannan

Abu ya girma: Majalisar dinkin duniya ta shiga lamarin sace dalibai a Neja

Gwamnati da hukumomin tsaro sun sha alwashin cewa ba za su runtsa ba har sai sun tabbatar da ceto wadanda aka sace cikin koshin lafiya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com