Mutane Sun Ga Abin da ba Su Taba Gani ba bayan Maida Nnamdi Kanu gidan Yarin Sakkwato

Mutane Sun Ga Abin da ba Su Taba Gani ba bayan Maida Nnamdi Kanu gidan Yarin Sakkwato

  • An tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen gidan yarin Sakkwato bayan labari ya bulla cewa an kai shugaban IPOB, Nnamdi Kanu
  • Wannan na zuwa ne bayan babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta yanke wa jagoran 'yan aware hukuncin daurin rai da rai
  • Mazauna Sakkwato sun bayyana cewa sun ga shigowar dakarun sojojin Najeriya da yawa, lamarin da suka ce ba su taba gani ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto, Nigeria - Mutanen gari sun ga sauyi a matakan tsaro bayan maida shugaban kungiyar 'yan Biafra watau IPOB, Nnamdi Kanu gidan yarin Sakkwato.

Rahoto ya nuna cewa an ƙara tsaurara matakan tsaro a gidan gyaran halin aka kai Kanu a jihar Sakkwato bayan babbar kotun tarayya ta yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta bada umarnin rufe makarantu 47 a fadin Najeriya

Nnamdi Kanu.
Hoton shugaban IPOB, Nnamdi Kanu a harabar Kotu a Abuja Hoto: @Ayofe
Source: Twitter

Tashar Channels ta ruwaito cewa an yanke wa Kanu hukuncin ɗaurin rai da rai ne ranar Alhamis a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, bayan an same shi da laifuka masu alaƙa da ta'addanci.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A hukuncin, Mai Shari'a James Omotosho ya umurci a mayar da Kanu zuwa “gidan yari mai talsaro," yana mai cewa Gidan Gyaran Hali na Kuje da ke Abuja ba shi da aminci.

Idan ba ku manta ba gidan yarin Kuje, wanda galibi aka fi tura manyan mutane na fama da matsaloli ciki har da hare-haren fashin magarkama daga 'yan ta'adda.

An maida Nnamdi Kanu Sakkwato

A ranar Juma’a, lauyansa, Alloy Ejimakor, ya shaida wa jaridar Punch cewa an mayar da Kanu gidan yarin Sakkwato.

Ya bayyana matukar damuwa kan wannan mataki saboda a cewarsa hakan ya nesanta jagoran IPOB daga tawagar lauyoyinsa, iyalinsa, da magoya bayansa.

Ejimakor ya yi kira ga ’yan kabilar Igbo da su kwantar da hankalinsu, ka da su yi kokarin aikata abin da ya karya doka.

Kara karanta wannan

Birnin Shehu ya yi baƙo, DSS ta maida Nnamdi Kanu Sokoto, zai zagaye Najeriya

An jibge jami'an tsaro a gidan yari

Sai dai jami’an gidan gyaran hali na Sokoto sun ƙi tabbatar da zuwansa, amma rahotanni sun nuna an ga dakarun tsaro fiye da kowane lokaci a wajen, tsaro ya yi tsauri fiye da da.

Bincike ya nuna cewa an girke jami’an tsaro dauke da makamai a muhimman wurare a ciki da wajen gidan yari.

Babbar motar dakon sojoji ta shiga harabar gidan gyaran halin, abin da ba kasafai yake faruwa ba.

Gidan gyaran hali.
Hoton hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Najeriya Hoto: @CorrectionsNG
Source: Twitter

Mutanen Sakkwato sun yi mamaki

Wani mazaunin yankin ya ce:

“Mun ga sojoji sun shigo da manyan motocinsu a yammacin yau, ba mu taba ganin irin wannan tsaro ba.”

Mai magana da yawun Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, Jane Osuji, ta tabbatar cewa Kanu yana hannunsu, amma ta ƙi bayyana ainihin wurin da ake tsare da shi saboda “yanayin da lamarin ya kunsa.”

'Yan Majalisa 44 sun roki a saki Kanu

A wani rahoton, kun ji cewa 'yan Majalisar Wakilai 44 sun fara kokarin lallaba Bola Ahmed Tinubu domin ya saki shugaban kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu.

Kara karanta wannan

Bidiyon Nnamdi Kanu yana rusa kuka a kotu ya ja hankalin jama'a

Rahoto ya nuna cewa yan Majalisar sun aika wasika ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, suna rokon ya ba da umarnin sakin Nnamdi Kanu nan take.

Sun kuma shawarci shugaban kasa da ya fara tattaunawar siyasa mai faɗi domin warware matsalolin tsaro da siyasar Kudu maso Gabas.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262