Gwamnatin Tinubu Ta Bada Umarnin Rufe Makarantu 47 a fadin Najeriya

Gwamnatin Tinubu Ta Bada Umarnin Rufe Makarantu 47 a fadin Najeriya

  • Gwamnatin tarayya ta ba da umarnin kulle makarantu 47 yayin da sha'anin tsaro ke kara tabarbarewa a wasu sassan Najeriya
  • Wannan mataki ne kunshe ne a wata sanarwa da ma'aikatar ilimi ta tarayya ta fitar yau Juma'a, 21 ga watan Nuwamba, 2025
  • A cikin wannan makon ne 'yan bindiga suka kai farmaki makarantu biyu a jihohin Neja da Kebbi, inda suka yi garkuwa da dalibai da malamai

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gwamnatin tarayya na ci gaba da daukar matakan kare rayuka da dukiyoyin 'yan Najeriya yayin da matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a kasa.

Wannan na zuwa ne bayan wasu jerin hare-hare da 'yan bindiga suka kai kan dalibai da masu ibada a jihohin Kwara, Neja da kuma Kebbi.

Ministan ilimi, Tunji Alausa.
Hoton Ministan Harkokin Ilimi, Dr. Tunji Alausa Hoto: @drtunjialausa
Source: Facebook

Gwamnatin Tarayya ta rufe makarantu 47

Kara karanta wannan

Matawalle ya yi bayani bayan gano wurin da aka boye 'daliban da aka sace a Kebbi

The Cable ta rahoto cewa a kokarin kare rayukan dalibai, Gwamnatin Tarayya ta ba da umarnin rufe makarantu 47 daga cikin wadanda ke karkashinta na ƙasar nan cikin gaggawa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matakin na zuwa ne biyo bayan abin da ke faruwa a wasu sassan ƙasar da kuma bukatar tabbatar da cewa ba a samu wata matsalar tsaro da za ta iya jefa rayuwar ɗalibai cikin hadari ba.

A cewar wata takardar sanarwa da ma'aikatar ilimi ta fitar a ranar Juma’a, 21 ga watan Nuwamba, 2025, Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya ba da umarnin rufe makarantun.

Sanarwar na dauke da sa hannun Binta Abdulkadir, Daraktar Sashen Makarantu na Sakandare na tarayya a madadin ministan.

Sunayen makarantun da aka rufe

Ta umurci dukkan shugabannin makarantu da abin ya shafa da su bi umarnin nan take ba tare da wani jinkiri ba, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

Makarantun da gwamnatin ta umarci a rufe su nan take sun hada da:

1. FGGC Minjibir

2. FTC Ganduje

3. FGGC Zaria

4. FTC Kafanchan

5. FGGC Bakori

6. FTC Dayi

7. FGC Daura

Kara karanta wannan

Mutane sun ga abin da ba su taba gani ba bayan maida Nnamdi Kanu gidan yarin Sakkwato

8. FGGC Tambuwal

9. FSC Sakkwato

10. FTC Wurno

11. FGC Gusau

12. FGC Anka

13. FGGC Gwandu

14. FGC Birnin Yauri

15. FTC Zuru

16. FGGC Kazaure

17. FGC Kiyawa

18. FTC Hadeja

19. FGGC Bida

20. FGC New Bussa

21. FTC Kuta–Shiroro

22. FGA Suleja

23. FGC Ilorin

24. FGGC Omu-Aran

25. FTC Gwanara

26. FGC Ugwolawo

27. FGGC Kabba

28. FTC Ogugu

29. FGGC Bwari

30. FGC Rubochi

31. FGC Abaji

32. FGGC Kazaure

33. FGC Kiyawa

34. FTC Hadejia

35. FGGC Potiskum

36. FGC Buni Yadi

37. FTC Gashua

38. FTC Michika

39. FGC Ganye

40. FGC Azare

41. FTC Misau

42. FGGC Bajoga

43. FGC Billiri

44. FTC Zambuk

45. FTC Ikare-Akoko

46. FTC Ijebu-Imusin

47. FTC Ushi-Ekiti.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Hoton shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

An rufe makarantun gwamnati a Katsina

A wani rahoton, kun ji cewa Gwamna Dikko Umaru Radda ta umarci a rufe dukkan makarantun firamare da sakandire na gwamnati da ke fadin jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Shugaban Amurka, Trump ya kara daukar zafi, ya kira Najeriya da kalma mara dadin ji

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da ma'aikatar kula da harkokin ilimin firamare da sakandire ta jihar Katsina ta fitar ranar Juma'a.

Ma’aikatar ta ja hankalin iyaye, malamai da al’umma gaba ɗaya da su bi wannan umarnin nan take, yayin da ake ci gaba da bibiyar yanayin tsaron jihar baki ɗaya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262