EFCC Ta Bayyana Wasu Yan Kasuwa da Ake Zargi da Daukar Nauyin Ta'addanci a Najeriya

EFCC Ta Bayyana Wasu Yan Kasuwa da Ake Zargi da Daukar Nauyin Ta'addanci a Najeriya

  • Shugaban EFCC, Ola Olukoyede ya ce wasu dillalan hakar ma'adanai da duwatsu masu daraja na da hannu a ayyukan ta'addanci a Najeriya
  • Olukoyede ya ce ana amfani da wasu yan kasuwa da ke harkar ma'adanai wajen safarar kudin haram da taimakawa 'yan ta'adda
  • Ya gargadi yan kasuwa da su guji mu'amala da wadanda suke da shakku a kansu, kuma su rika ba da rahoton don taimakon hukumomi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ibadan, Oyo State – Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) ta bankado wasu manyan dillalai da take zargin suna da hannu a daukar nauyin ta'addanci a Najeriya.

Kara karanta wannan

Kungiyar Amnesty Int'l ta yi magana da Hisbah ta kama masu shirin 'auren jinsi' a Kano

EFCC ta ce wasu ‘yan kasuwa da masu sana’ar haka da cinikayyar duwatsu da ma’adinai masu daraja na daga cikin wadanda ke daukar nauyin ayyukan ta’addanci a wasu yankunan kasar nan.

Shugaban EFCC, Ola Olukoyede.
Hoton shugaban hukumar EFCC, Ola Olukoyede a wurin taro Hoto: @OfficialEFCC
Source: Facebook

Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin wani taron wayar da kai da horaswa na yini guda a Ibadan, cewar rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taron dai na shirya shi ne domin horas da masu hakar ma’adinai da ‘yan kasuwar duwatsu masu daraja a Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Bugu da kari, bayanai sun nuna cewa an shirya taron ne da hadin gwiwar EFCC da hukumar bayanan kudi ta kasa (NFIU), tare da tallafin hukumar kasar Jamus ta GIZ.

Shugaban EFCC ya fadi masu taimakon yan ta'adda

Olukoyede, ya yi jawabi a taron ta bakin wakilinsa, Toyin Ehindero-Benson, mai kula da sashen yaki da safarar kudi (SCUML) na ofishin EFCC a Ibadan.

Shugaban EFCC ya soki wasu ‘yan kasuwa da ke yin sakaci wajen bin ka’idojin sanin abokan hulɗarsu wajen cinikayyar ma'adanai da duwatsu masu daraja.

Kara karanta wannan

ADC ta aika sako mai zafi ga Tinubu kan sauya hafsoshin tsaro

Ya ce, rashin bin doka da rashin bayar da rahoton mu’amaloli da ake shakku a kansu na daga cikin dalilan da ke kawo cikas ga yunkurin EFCC na yaki da safarar kudi da daukar nauyin ta’addanci.

EFCC ta gargadi masu harkar ma'adanai

Olukoyede, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun EFCC, Dele Oyewale, ya fitar, ya ce:

“Ayyukan wannan masana’anta (ma’adinai) yana da muhimmanci sosai wajen yaki da manyan laifukan kudi.
"Wannan taron ya ba mu damar fadakarwa, musayar dabaru, da karfafa hadin kai tsakanin hukumomi da masu sana’a,” in ji

Ya kuma gargadi masu hakar ma’adinai da ‘yan kasuwar duwatsu masu daraja da su guji bari a yi amfani da su wajen safarar kudaden haram da daukar nauyin ayyukan ta’addanci, kamar yadda PM News ta rahoto.

Shugaban EFCC na kasa.
Hoton shugaban hukumar EFCC na kasa, Ola Olukoyede Hoto: EFCC Nigeria
Source: Facebook

EFCC ta kwato Naira biliyan 500

A wani rahoton, kun ji cewa mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana nasararorin da hukumar yaki da cin hanci ta EFCC ta samu a karkashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Shettima ya ce EFCC ta samu nasarar tara dukiyar da ta kai Naira biliyan 500 cikin shekaru biyu da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi a kan mulki.

Kara karanta wannan

Jagororin PDP sun rabu a kan bai wa turaki shugabancin jam'iyya

Ya ce manufar gwamnatin Tinubu ta rashin tsoma baki a harkokin hukumomin yaki da rashawa ta taimaka wajen karfafa yaki da cin hanci da kuma inganta gaskiya a hukumomin gwamnati.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262