Bola Tinubu Ya Kira Sababbin Hafsoshin Tsaro, Sun Shiga Ganawa a Aso Rock

Bola Tinubu Ya Kira Sababbin Hafsoshin Tsaro, Sun Shiga Ganawa a Aso Rock

  • Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci taron tsaro na farko bayan sauya manyan hafsoshin tsaron Najeriya
  • Rahotanni daga fadar shugaban kasa sun tabbatar da cewa sabbabin hafsoshin tsaron kasar nan sun halarci taron yau Litinin, 27 ga Oktoba, 2025
  • Duk da babu wata sanarwa a hukumance da ta bayyana abubuwan da aka tattauna, amma majiyoyi sun ce zaman maida hankali kan tsarin tsaro

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Najeriya – Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya shiga taron sirri da sababbin hafsoshin rundunonin sojojin Najeriya a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Bulama Bukarti ya kawo mafita ga Najeriya maimakon sauya hafsoshin tsaro

Har kawo yanzu babu wani cikakken bayani kan abubuwan da za a tattauna a wannan taron tsaro, karo na farko bayan Tinubu ya sauya manyan hafsoshin tsaron Najeriya.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Hoton shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya da ke Abuja Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

Bola Tinubu ya gana da hafsoshin tsaro

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa majiyoyi sun nuna cewa ganawar na da nasaba da ƙoƙarin da ake yi don ƙarfafa tsarin tsaro da inganta aikin rundunonin sojoji a ƙasar nan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Manyan hafasoshin tsaron lasar nan sun halarci wannan taro wanda ke gudana yanzu haka a Aso Rock, yau Litinin, 27 ga watan Agusta, 2025.

Fadar shugaban ƙasa dai ta bayyana cewa nadin sababbin hafsoshin tsaro wani muhimmin mataki ne na inganta tsarin tsaro da ayyukan rundunonin tsaro na Najeriya.

Hafsoshin tsaron da suka halarci taron

Rahotanni sun nuna cewa wadanda suka halarci wannan taron sun haɗa da; Babban Hafsan Tsaro na Kasa, Janar Olufemi Oluyede da Babban Hafsan Rundunar Sojojin Kasa, Manjo Janar Waidi Shaibu.

Haka zalika an ga Babban Hafsan Rundunar Sojojin Sama, Air Vice Marshal Kennedy Aneke Babban Hafsan Rundunar Sojojin Ruwa ta Najeriya, Rear Admiral Idi Abbas sun shiga wannan taro.

Kara karanta wannan

Dalilin Buhari da Tinubu na korar Janar 500 daga rundunar tsaro duk da matsalar ta'addanci

Ana sa ran ganawar za ta mayar da hankali kan tsare-tsaren tsaro, dabarun yaki da ta’addanci da kuma hanyoyin inganta haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a ƙasar nan.

Dalilan sauya hafsoshin tsaron Najeriya

Wannan ci gaban ya zo ne ‘yan kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya yi sauye-sauye a manyan hafsoshin sojojin kasar nan, cewar rahoton Channels tv.

A cikin wannan sauyi, Tinubu ya sauke Janar Christopher Musa daga mukaminsa na Babban Hafsan Tsaro, inda ya nada Janar Olufemi Oluyede, wanda a da shi ne Babban Hafsan Sojojin Kasa.

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai, Sunday Dare, ya tabbatar da wannan sauyi, yana mai cewa matakin yana cikin kokarin gwamnatin tarayya na karfafa tsarin tsaron kasa.

Shugaba Tinubu da hafsoshin tsaro.
Manyan hafsoshin tsaro tare da Shugaba Tinubu a fadar gwamnatin tarayya Hoto: @Sundaydare
Source: Twitter

Babban mai bincike ya yaba wa Tinubu

A wani rahoton, kun ji cewa babban mai bincike a matakin duniya, Oyewole Oginni, ya bayyana cewa sauya manyan hafsoshin tsaro ba abin tada hankali ba ne.

Oginni, babban mai bincike a Cibiyar Nazarin Rikice-rikice ta Duniya da ke Bonn, da ke Jamau ya ce duba da abubuwan da faruwa, Bola Tinubu ya yi abin da ya dace kuma akan lokaci.

Kara karanta wannan

Sarki Sanusi II zai jagoranci taron duniya a gaban gwamnoni da ministoci

Ya bayyana cewa duba da yadda wasu ƙasashen Afirka ke fadawa mulkin soja, da yadda ’yan ta’addan ISWAP ke matsowa Kudu a Najeriya, akwai bukatar sauya tsarin tsaron kasar nan.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262