Bayan Kirkirar Sababbin Masarautu, Gwamna Ya Nada Yayansa Sarki a Bauchi

Bayan Kirkirar Sababbin Masarautu, Gwamna Ya Nada Yayansa Sarki a Bauchi

  • Gwamna Bala Mohammed na Bauchi ya nada sababbin sarakuna a jihar bayan kirkirar masarautu a kwanakin nan
  • Sanata Bala Mohammed ya naɗa ɗan’uwansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sabon Sarkin masarautar Duguri
  • A wurin bikin miƙa takardar naɗe, sabon Sarkin Duguri da na Bununu sun gode wa Gwamna Bala tare da alƙawarin bin doka da goyon bayan gwamnati

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Bauchi - Gwamna Bala Mohammed na Bauchi ya naɗa sababbin sarakunan gargajiya a jihar bayan kirkirar karin masarautu a kwanan nan.

Gwamnan ya nada babban yayansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sabon Sarkin masarautar Duguri da aka ƙirƙira kwanan nan.

Gwamna ya nada yayansa sarauta a Bauchi
Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi yayin taro a Abuja. Hoto: Senator Bala Abdulkadir Mohammed.
Source: Facebook

Daily Trust ta ce sakataren gwamnatin jihar, Aminu Hammayo, ne ya mika takardar naɗe a madadin Gwamnan a fadar Sarkin Duguri.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: An kama dalibin jami'ar IBB kan saboda gwamna a Facebook

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna Bala ya kirkiri sababbin masarautu

Hakan na zuwa ne bayan gwamnan jihar ya kirkiri sababbin masarautu domin inganta shugabanci da samar da ingantaccen shugabanci.

Gwamna Bala Mohammed ya sanya hannu kan dokar sababbin masarautu 13 da hakimai 111 a fadin jihar Bauchi.

Ya kuma soke tsohuwar masarautar Sayawa, ya kafa masarautar Zaar da hedkwatarta a Mhrim Namchi, Tafawa Balewa, cewar rahoton The Guardian.

Har ila yau, gwamnan ya gargadi masu siyasantar da doka, ya kuma rattaba hannu kan dokar fansho da karin kasafin kudi na 2025.

Gwamna Bala ya bukaci hadin kai daga sarakuna
Gwamna Bala Mohammed yayin taro a gidan gwamnatin Bauchi. Hoto: Sen. Bala Abdulkadir Mohammed.
Source: Facebook

An yi bikin nadin sababbin sarakuna a Bauchi

An gudanar da nadin a Masarautar Duguri na cikin karamar hukumar Alkaleri a ranar Juma’a 24 ga watan Oktobar shekarar 2025 da muke ciki.

A wajen taron, Hammayo ya roƙi sabon Sarkin da ya ci gaba da mara wa shirye-shiryen gwamnati baya domin cigaban al’umma da dorewar zaman lafiya.

Sabon Sarkin Duguri, ya gode wa Gwamna Bala bisa wannan karamci, yana roƙon Allah ya saka masa da alheri tare da yin alƙawarin biyayya ga gwamnati.

Kara karanta wannan

Injiniyoyi sun ga kokarin Gwamna Abba, sun ba shi lambar girmamawa

Sarkin Bununu ya karbi takardar nadin sarauta

Haka kuma, Sakataren Gwamnatin ya mika takardar naɗi ga sabon Sarkin masarautar Bununu, Alhaji Jibrin D. Hassan, wanda aka nada su a lokaci guda.

Hammayo ya shawarci sabon Sarkin Bununu da ya tabbatar da bin doka, haɗin kai tsakanin kabilu da samar da zaman lafiya a yankinsa.

Sabon Sarkin Bununu ya gode wa Gwamna Bala bisa amincewa da shi, yana mai tabbatar da cewa ba zai taɓa rusa amanar gwamnati da jama’a ba.

Gwamna Bala ya musanta fita daga PDP

Mun ba ku labarin cewa Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya tabo batun yiwuwar ficewa daga jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya.

Shugaban na kungiyar gwamnonin PDP, ya yi nuni da cewa ba zai iya ficewa daga jam'iyyar ta adawa ba inda ya ba yan jam'iyyar tabbaci kan inganta ta.

Gwamna Bala ya nuna cewa akwai hannun wasu kan kokarin kawo rarrabuwar kawuna a jam'iyyar PDP domin farraka ta wanda ya ce za su yi duk mai yiwuwa don dakile haka.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.