Gwamnoni 19 Sun Hada Baki Sun Yi Magana kan Mutuwar Sama da Mutane 40 a Jihar Neja

Gwamnoni 19 Sun Hada Baki Sun Yi Magana kan Mutuwar Sama da Mutane 40 a Jihar Neja

  • Gwamnonin Arewa sun yi alhinin rayukan da aka rasa a mummunan hatsarin tankar mai da ya faru a jihar Neja
  • Shugaban kungiyar gwamnonin Arewa kuma gwamnan Gombe, Inuwa Yahaya ya mika sakon ta'aziyya ga iyalai da gwamnatin Neja
  • Ya bukaci jama'a su hada kai da gwamnati da hukumomin tsaro domin daukar matakan hana sake faruwar irin wannan bala'i a gaba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Minna, Jihar Neja – Gwamnonin Arewa 19 karkashin kungiyarsu ta Northern States Governors’ Forum (NSGF) sun nuna damuwa kan fashewar tanka a jihar Neja.

Gwamnonin sun bayyana babban alhini da bacin rai bisa ibtila'in fashewar tankar man fetur da ya faru a kauyen Essa da ke cikin karamar hukumar Katcha ta jihar Neja.

Gwamna Inuwa Yahaya na jihar Gombe.
Hoton Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na jihar Gombe Hoto: Mohammed Inuwa Yahaya
Source: Facebook

Tashar Channels tv ta tattaro cewa adadin mutanen da suka mutu a fashewar tanka a jihar Neja sun kai 42, wasu sama da 60 sun jikkata.

Kara karanta wannan

'Dan Najeriya ya yi amfani da kayan aikin mace, ya burma kansa a matsala a Ingila

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnonin Arewa aika sako ga Bago

Gwamnonin jihohi 19 da ke Arewacin Najeriya sun yi jimami da ta'aziyya ga iyalan wadanda suka mutu a wannan mummunan lamari da ya faru jiya Talata.

Shugaban kungiyar kuma Gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana bakin ciki matuƙa kan wannan bala’i da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama da raunata wasu.

A madadin gwamnonin Arewa, Inuwa Yahaya ya mika ta’aziyya ga Gwamnan Neja, Mohammed Umar Bago, da mutanen jihar baki ɗaya, musamman iyalan da suka rasa ’yan uwansu a wannan mummunan lamari.

Daily Trust ta rahoto Gwamna Inuwa na cewa:

“Wannan lamari abin takaici ne kuma mai zafi ƙwarai. Zuciyarmu tana tare da iyalan da suka rasa ’yan uwansu da dukkan jama’ar jihar Neja a wannan lokaci na jimami.”

An gargaji mutane kan dibar mai daga tanka

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun bude wa mota wuta, sun yi awon gaba da ma'aikatan INEC a Kogi

Gwamna Inuwa ya gargaɗi jama’a da su guji taruwa ko diban mai lokacin da irin waɗannan hatsarori suka faru, yana mai cewa hakan na iya jawo ƙarin asarar rayuka.

"Wannan abu ya sake tunatar da mu muhimmancin ɗaukar matakan tsaro da wayar da kai game da haɗarin sufuri da jigilar kayan fashewa.
"Ya zama wajibi gwamnati, hukumomin da ke kula da harkar tsaro da kuma jama’a su haɗa kai domin hana irin waɗannan abubuwan faruwa nan gaba.”
Gwamnonin Arewa.
Hoton wasu daga cikin gwamnonin Arewa a wurin taron da suka gudanar a Kaduna Hoto: Uba Sani
Source: Facebook

Gwamnan ya kuma yaba da ƙoƙarin jami’an ceto, ’yan sanda da ma fararen hula da suka shiga aikin ceto wadanda suka tsira da bayar da taimako cikin gaggawa.

A ƙarshe, Inuwa Yahaya ya yi addu’a ga Allah ya jikan waɗanda suka rasu tare da neman waraka ga waɗanda suka jikkata.

Yadda tanka ta fashe a jihar Neja

A wani labarin, kun ji cewa wata tanka makare da mai ta fashe a kan titin Agaie zuwa Bida a jihar Neja da yammacin Talata, 21 ga watan Oktoba, 2025.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya haddasa cunkoson ababen hawa mai tsanani a babbar hanyar, inda motoci suka makale na sa’o’i da dama.

Kara karanta wannan

Gwamna ya bi sahun Peter Mbah ya koma jam'iyyar APC mai mulki? Gaskiya ta bayyana

Hukumar Kiyaye Hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Neja ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce mutane da dama sun rasa rayukansu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262