Lokaci Ya Yi: Malamin Addinin Musulunci a Kano kuma Na'ibin Masallacin Al Furqan Ya Rasu
- Na'ibin Sheikh Bashir Aliyu Umar a masallacin Jumma'a na Al-Furqan Kano, Malam Aminu Adam Dorayi ya riga mu gidan gaskiya
- Dr. Bashir Aliyu ya tabbatar da rasuwar malamin yau Talata, 21 ga watan Oktoba, 2025, ya ce za a yi jana'izarsada misalin karfe 10:00 na safe
- Tuni dai mabiya da sauran al'ummar musulmi a Kano suka fara jaje da ta'aziyyar rasuwar Malam Aminu Adam, wanda aka bayyana da mutumin kirki
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Kano - Malamin addinin musulunci a jihar Kano, Malam Aminu Adam ya riga mu gidan gaskiya.
Marigayi Malam Aminu na daya daga cikin limamanin babban masallacin Jumma'a na Al-Furqan da ke cikin birnin Kano.

Source: Facebook
Fitaccen malamin addinin musuluncin kuma shugaban Majalisar Shari'a ta Najeriya, Dr. Bashir Aliyu Umar ne ya tabbatar da rasuwar Malam Aminu Adam a shafinsa na Facebook.
Dr. Bashir Aliyu Umar shi ne babban limamin masallacim Al-Furqan da ke Alue Avenue a cikin garin Kano.
Na'ibin masallacin Al-Furqan Kano ya rasu
A sanarwar da ya wallafa yau Talata, 11 ga watan Oktoba, 2025, Sheikh Bashir Aliyu ya ce Malam Aminu Adam shi ne na'ibinsa masallacin Jumma'a na Al-Furqan Kano.
Sanarwar ta ce za a yi jana'izar marigayin kamar yadda addinin musulunci ya tanada da misalin karfe 10:00 na safiya a masallacin Al-Muntadha da ke Dorayi (masallacin marigayi Sheikh Ja'afar Mahmud Adam).
Tuni dai mutane musamman jama'ar Kano suka fara tura sakon ta'aziyya da addu'ar Allah Ya jikan Malam Aminu Adam kuma ya gafarta masa kura-kuransa
An sanar da lokacin jana'izar malamin
Sanarwar ta ce:
"innalilLahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah Ya yi wa Dan'uwa Mal. Aminu Adam Rasuwa, shi ne Na’ibin Limamin Juma’a na Masallacin Al-Furqan Kano.
"Za a yi Jana’izarsa da Karfe 10:00 na safe (yau Talata, 21 ga watan Oktoba, 2025) a Masallacin Al-Muntada Dorayi watu Masallacin marigayi Mal. Ja’afar Mahmud Adam."
Sheikh Daurawa ya mika sakon ta'aziyya
Babban kwamandan Hisbah na jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawaya yi ta'aziyyar rasuwar Malam Aminu a shafinsa na Facebook.
Sheikh Daurawa ya ce Malam Aminu ya kasance abokinsu na da'awah, mutumin kirki, ga haƙuri ga iya mu'amala, Idan yana nasiha ko khuɗuba yana yawan tunasar da mutane game da mutuwa.
"Muna addu'a Allah ya masa rahama. Allah ya yafe masa kura-kuransa. Allah ya mi shi tukwuici da aljannar Firdausi, Ya kuma bawa iyalinshi haƙurin jure wannan babban rashi da muka yi.
"Ina mika ta'aziyyata ga ɗaukacin al'ummar Musulmai, da Dr Bashir Aliyu."

Source: Facebook
Malam Kabiru Madabo ya rasu a Kano
A wani labarin, kun ji cewa fitaccen malamin addinin musulunci a Kano, Malam Kabiru Ibrahim Madabo, ya kwanta dama.
Sheikh Anas Mahmud Madabo ne ya tabbatar da rasuwar malamin, yana bayyana cewa al’umma sun yi babban rashi a bangaren ilimi.

Kara karanta wannan
Jam'iyyar PDP da sakatarenta na ƙasa sun samu sabani kan takardar da aka aika wa INEC
Wannan mutuwa ta taba al'ummar Kano yayin da mutane da dama ke jimamin rasuwar tasa da kuma yi masa addu'ar samun rahama.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

