'Yan Bindiga Sun Sace Mutane kusan 100 a Wasu Kauyukan Zamfara

'Yan Bindiga Sun Sace Mutane kusan 100 a Wasu Kauyukan Zamfara

  • 'Yan bindiga sun yi awon gaba da mutanen da ba su san hawa ba, ba su sauka ba a jihar Zamfara bayan sun kai wasu hare-hare
  • Miyagun 'yan bindigan sun sace mutanen ne a wasu kauyuka guda biyu na karamar hukumar Bukkuyum bayan sun farmake su a cikin dare
  • Jami'an tsaro sun fara kokarin ganin sun kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su zuwa cikin daji domin ganin an sada su da iyalinsu

​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Zamfara - 'Yan bindiga sun yi awon gaba da akalla mutane 73 yayin wasu hare-hare a jihar Zamfara

'Yan bindigan sun sace mutanen ne bayan hare-haren da suka kai kauyukan Buzugu da Rayau a cikin karamar hukumar Bukkuyum ta jihar Zamfara.

'Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane a Zamfara
Jami'an rundunar 'yan sanda a bakin aiki Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Masani kan harkokin tsaro a yankin Tafkin Chadi da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Yadda yan sanda suka dakume 'yan jaridan Faransa 2 a zanga zangar Nnamdi Kanu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

'Yan bindiga sun kai hare-hare a Zamfara

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:45 na daren ranar Asabar, 18 ga watan Oktoban 2025.

'Yan bindigan waɗanda suka zo da yawa kuma ɗauke da makamai masu haɗari, sun mamaye kauyukan biyu tare da yin awon gaba da mazauna yankin zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Miyagun sun rika harbin iska don tsoratar da jama’a, kafin daga bisani su shiga gidaje suna tattara mutane cikin firgici.

Bayan sun gama da kauyen Buzugu, daga nan suka wuce Rayau, inda suka sake kama mutane da dama, ciki har da mata da yara, sannan suka nufi da su cikin daji.

An fara yunkurin ceto mutanen da aka sace

Wata majiya daga jami’an tsaro ta tabbatar da cewa an tura sojoji da ‘yan sa-kai zuwa yankin domin bin sawun masu garkuwa da mutane tare da ceto waɗanda aka sace.

"An riga an kaddamar da bincike mai zurfi domin gano inda ‘yan bindigan suka kai mutanen da suka sace. Hukumomin tsaro suna aiki tare da ‘yan sa kai na yankin domin tabbatar da cewa an dawo da zaman lafiya cikin gaggawa.”

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi awon gaba da mutanen da suka fita neman na kansu a Zamfara

- Wata majiya

Mummunan harin ya jefa mazauna yankin cikin tsananin tsoro da rudani, inda da dama daga cikinsu suka tsere zuwa kauyukan da ke makwabtaka da su don neman mafaka.

Jami’an tsaro sun tabbatar wa al’umma cewa suna kara kaimi wajen ayyukan tsaro, tare da haɗin gwiwa da sauran hukumomi da kungiyoyin ‘yan sa-kai, domin dawo da kwanciyar hankali a yankin.

'Yan bindiga sun sace mutane masu yawa a Zamfara
Taswirar jihar Zamfara, tarayyar Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga

'Yan bindiga sun sace mahauta a Zamfara

A wani labarin kuma, kun ji cewa 'yan bindiga dauke da makamai sun yi garkuwa da wasu mahauta da dillalan dabbobi a Zamfara.

Tsagerun 'yan bindigan sun sace mutanen ne lokacin da suke kan hanyar komawa gida bayan sun halarci wata kasuwa a karamar hukumar Gusau.

Kara karanta wannan

An shiga tashin hankali: 'Yan bindiga da makiyaya sun mamaye gari guda a Benue

'Yan uwan mutanen da aka sace sun bayyana cewa 'yan bindigan sun kira domin a kai kudin fansan daya daga cikinsu ko kuma su kashe shi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng