Asiri Ya Tonu, an Kama Hatsabiban Yan Bindiga da Suka Hallaka Sarki Mai Martaba

Asiri Ya Tonu, an Kama Hatsabiban Yan Bindiga da Suka Hallaka Sarki Mai Martaba

  • Jami’an tsaro sun cafke wasu manyan hatsabiban ‘yan ta’adda biyu tare da masu daukar nauyinsu, inda aka kwato bindigogi, harsasai
  • Daya daga cikin wadanda aka kama, Paschal Ibuaku, ya amsa laifin shiga ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da kuma kisa
  • An kuma kama wasu mutane biyu da ake zargi da daukar nauyin kungiyar, Magnus Ejiogu da Miletus Ihueze

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Owerri, Imo - Jami’an tsaro sun samu galaba kan miyagun yan bindiga inda suka samu manyan makamai wanda suke amfani da su domin kai hare-hare.

Jami'an a jihar Imo sun yi nasarar cafke manyan hatsabiban ‘yan ta’adda biyu tare da masu daukar nauyinsu bayan wani samame da suka kai a wasu kananan hukumomi.

Jami'an tsaro sun kama yan bindiga da kuma wanda ya kashe Sarki
Babban ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar. Hoto: Defence Headquarters Nigeria.
Source: Facebook

Rahoton Zagazola Makama ya tabbatar da haka a shafin X inda ya ce an kwato bindigogi, harsasai da kayan tsafi daga hannunsu.

Kara karanta wannan

Ta tabbata, sojojin Najeriya sun kama hatsabibin ɗan ta'adda da aka jima ana nema

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda yan bindiga ke kai hare-hare a Imo

Jihar Imo na daga cikin jihohin Kudu maso Gabas a Najeriya da suke shan fama da matsalolin tsaro.

A baya, gwamnatin jihar Imo ta yi alkawarin yin duk abin da ya dace don ganin ta ceto Ngozi Ogbu, tsohon ɗan majisa da aka sace.

A ranar 7 ga Satumba, 2025 ne wasu da ake zargin 'yan kungiyar IPOB ne, ɗauke da makamai suka sace Mista Ngozi.

Wadanda suka sace tsohon dan majalisar, sun ce za su kashe shi idan gwamnati ba ta biya bukatunsu a kwanaki hudu ba.

Jami'an tsaro sun kama manyan yan bindiga
Taswirar jihar Imo da ke Kudu maso Gabashin Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Wadanda aka kama kan zargin ta'addanci a Imo

Majiyoyi sun nuna cewa an kama daya daga cikin su, Paschal Ibuaku, a Obudi Agwa yayin da yake daukar sababbin ‘yan kungiyar IPOB/ESN.

Ya amsa laifin shiga ta’addanci, fashi, garkuwa da mutane da kisan kai, ciki har da kashe Sarkin Agwa, Eze Dr. I.O. Asor, a ranar 14 ga Oktoba, 2022.

Kara karanta wannan

Sabon rikici ya barke a wani yankin Kaduna, an kashe fiye da mutane 5 a rana 1

Haka kuma, an cafke wasu mutane biyu da ake zargin sun dauki nauyin ta’addancin, Magnus Ejiogu da wani boka mai suna Miletus Ihueze.

Matakan da jami'an tsaro suka dauka kan lamarin

Ejiogu ya biya Naira miliyan daya domin kashe Sarkin, yayin da Ihueze ya bayar da miliyan hudu da taimakon tsafi saboda rikicin fili.

Jami’an tsaro sun ce ana cigaba da bincike kan wadanda aka kaman, kuma wadanda suka tsere za a kamo su.

Yan bindia sun yi barna a Katsina

Mun ba ku labarin cewa ‘yan bindiga a Katsina sun kai wani hari a jihar ta wani irin sabon salo wanda ya jawo asarar dukiyoyi bayan kakaba haraji kan manoma da suke shirin girbe amfanin gona.

An tabbatar da cewa maharan tara shanun sata sama da 200, suka sako su cikin gonaki a karamar hukumar Kankia da ke jihar da ke Arewacin Najeriya.

Sun kuma bukaci mazauna Kada su biya kuɗin fansa ₦4m, tare da barazanar hana su girbi idan ba su biya ba wanda hakan ya yi matukar tayar da hankulan mazauna yankin.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.