Sardaunan Zazzau: Jonathan, Atiku, Obi Sun Taya Namadi Sambo Samun Sarauta

Sardaunan Zazzau: Jonathan, Atiku, Obi Sun Taya Namadi Sambo Samun Sarauta

  • Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Namadi Sambo, ya karɓi sarautar Sardaunan Zazzau daga Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli
  • Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Peter Obi sun taya shi murnar sabon sarautar da ya samu
  • Rahotanni sun bayyana cewa an gudanar da bikin nadin sarautar ne a fadar Sarkin Zazzau da ke Zariya ranar Asabar, 11 ga Oktoba, 2025

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kaduna – Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya karɓi sarautar Sardaunan Zazzau daga Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli.

Rahotanni sun bayyana cewa an yi bikin nadin sarautar ne a wani babban bikin da aka gudanar a fadar Sarkin Zazzau.

Sardaunan Zazzau, Namadi Sambo
Lokacin da aka nada Namadi Sambo Sardaunan Zazzau. Hoto: Zazzau Emirate
Source: Facebook

Bikin ya samu halartar fitattun mutane daga sassan Najeriya daban-daban, ciki har da tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan kamar yadda ya wallafa a X.

Kara karanta wannan

Bayan yin afuwa ga su Maryam Sanda, Tinubu ya bar Najeriya, ya shilla kasar waje

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jonathan ya taya Namadi murna

Tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan ya nuna farin cikin samun damar halartar nadin sarautar, inda ya bayyana Namadi Sambo a matsayin mutum mai gaskiya da kishin ƙasa.

A cikin sakon da ya wallafa, Jonathan ya ce:

“Na yi matuƙar farin ciki da kasancewa tare da ɗan’uwana mai girma, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, yayin bikin nadin sa a matsayin Sardaunan Zazzau.”

Ya ƙara da cewa sabon matsayin zai ƙara dankon zumuncinsa da al’umma tare da ƙarfafa sadaukarwarsa wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Peter Obi ya yaba wa Namadi Sambo

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi, ya bayyana nadin sarautar a matsayin wata gagarumar shaida ta yadda masarautar Zazzau ke girmama mutanen da suka ba da gudunmawa.

A cikin sakon da ya wallafa a X, Obi ya ce:

“Ina taya ɗan’uwana mai girma, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Namadi Sambo, murnar samun wannan sarauta mai daraja.

Kara karanta wannan

Sardaunan Zazzau: Tinubu ya taya Namadi Sambo murnar samun sarauta

"Nadin ya nuna amincewar masarautar da hikimarka, amincinka, da jajircewarka wajen ci gaban al’umma.”

Baya ga haka, Obi ya mika godiya ga Sarkin Zazzau bisa cigaba da girmama mutanen kirki a cikin al’umma.

Sardaunan Zazzau, Namadi Sambo
Namadi Sambo da aka nada Sardaunan Zazzau. Hoto: Masarautar Zazzau
Source: Facebook

Maganar Atiku da Abbas Tajudeen

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya taya Namadi Sambo murnar nada shi sarautar da aka yi a sakon da ya wallafa a X.

A sanarwar da ya fitar a X, Shugaban majalisar wakilai kuma Iyan Zazzau, Abbas Tajudeen ya taya Namadi Sambo murna bayan halartar taron.

Sanata Lawal Adamu ya taya Namadi murna

Sanata Lawal Adamu ma ya taya tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa murnar Sarautar da aka ba shi.

A cikin sakon da ya wallafa a X, ya ce:

“Ina taya tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Namadi Sambo murnar nadin sa a matsayin Sardaunan Zazzau. Allah Ya sanya alheri, Amin.”

Sanatan ya bayyana Namadi Sambo a matsayin mutum mai sadaukarwa da natsuwa wanda ya ba da gudunmawa sosai ga harkokin mulki da ci gaban al’umma.

Kara karanta wannan

Gwamna na shirin komawa APC, tsohon jagora a Majalisar Dattawa ya fice daga PDP

Tinubu ya taya Sardaunan Zazzau murna

A wani rahoton, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon mataimakin shugaban kasa murna zama Sardaunan Zazzau.

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa nadin sarautar ya nuna yadda Namadi Sambo ya kawo cigaba a lokacin da ya ke rike da madafun iko.

Shugaban kasar ya yaba wa masarautar Zazzau kan cigaba da girmama mutanen da suka yi wa kasa hidima wajen kawo cigaba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng