Hafsan Tsaro a Mulkin Buhari Ya Fadi Adadin Sojoji da Aka Kashe a Yakin Boko Haram

Hafsan Tsaro a Mulkin Buhari Ya Fadi Adadin Sojoji da Aka Kashe a Yakin Boko Haram

  • Tsohon hafsan tsaro a Najeriya, Janar Lucky Irabor ya bayyana yawan sojoji da aka hallaka a yaki da Boko Haram a Arewacin Najeriya
  • Irabor ya ce aƙalla sojoji 2,700 ne suka mutu cikin shekaru 12 na yaƙin da Najeriya ke yi da yan ta'addan Boko Haram wanda ya jawo asararar rayukan fararen hula
  • Tsohon hafsan tsaron ya ƙaryata zargin cewa sojoji daga wani addini ne kawai ake tura wa yanki mai haɗari inda ake rasa rayukansu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja - Tsohon Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Lucky Irabor (mai ritaya), ya bayyana adadin sojoji da suka mutu a yaki da Boko Haram.

Irabor ya bayyana cewa an rasa rayukan sojoji kusan 2,700 cikin shekaru 12 na yaƙin Boko Haram musamman a yankunan Borno, Yobe da jihar Adamawa.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Sojoji sun harbe ɗan sanda har lahira daga musayar yawu a Bauchi

An fadi yawan sojoji da aka hallaka a yaki da Boko Haram
Tsohon Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor mai ritaya. Hoto: HQ Nigerian Army.
Source: Facebook

Boko Haram: Irabor ya fadi adadin asarar rayuka

Ya bayyana haka ne cikin sabon littafinsa mai suna “SCARS: Nigeria’s Journey and the Boko Haram Conundrum” wanda Leadership ta bibiya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Janar Irabor ya ƙaryata zargin cewa sojoji daga wani addini ko ƙabila ne suka fi mutuwa a yaƙin, yana mai cewa asarar ta shafi kowa.

Ya kuma ambaci rahoton UNDP da ya nuna cewa rikicin Boko Haram ya yi sanadin mutuwar mutum kusan 350,000 zuwa shekarar 2020.

A cewarsa:

“Ziyartar makabartar sojoji na nuna cewa Musulmai da Kiristoci sun yi asara iri ɗaya, ba kamar yadda ake yaɗa jita-jita ba.”

Janar ɗin ya bayyana cewa yaƙin Boko Haram ya bar tabo ga Najeriya, yana kira ga ƙasar ta koya darasi da ƙarfafa haɗin kai.

Yawan sojoji da aka kashe a yaki da Boko Haram
Taswirar jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Zargin da Irabor ya yi kan wasu kungiyoyi

Irabor ya zargi rahotannin wasu ƙungiyoyi da suka rage ƙarfin gwiwar sojoji tare da ɓata suna a idon Amurka har aka yi wa wasu takunkumi.

Kara karanta wannan

Wasu daga cikin mutane 175 da Tinubu ya yi wa afuwa da laifin da suka aikata

Ya tuna cewa Amnesty International ta taɓa zargin sojojin Najeriya da kisan fararen hula, duk da rahoton gwamnati ya tabbatar babu gaskiya a ciki, cewar Punch.

Irabor ya bayyana cewa Janar Ngubane da Janar Bamigboye sun fuskanci wahala bayan ƙin basu 'visa' daga Amurka saboda waɗannan rahotanni.

Ya ce matsalolin tsaro a Arewacin ƙasa sun samo asali ne daga jahilci, talauci, da rikice-rikicen neman albarkatun ƙasa tsakanin manoma da makiyaya.

Haka kuma ya danganta matsalolin IPOB, Oduduwa, da rashin adalcin tattalin arziki a yankin Neja Delta da sakamakon gazawar tsaro a Najeriya.

Janar Irabor ya tuna wahalar da ya sha

Mun ba ku labarin cewa tsohon Hafsan tsaron Najeriya, Lucky Irabor ya yi magana kan kalubale da ya fuskanta a lokacin jagorancinsa a mulkin Muhammadu Buhari.

Irabor ya bayyana cewa harin jirgin kasa da aka kai na Abuja zuwa Kaduna a 2022 shi ne abu mafi wahala wanda ya rikita shi a lokacin jagorancinsa.

Tsohon hafsan tsaron ya ce ya rubuta littafi mai suna 'Scars. 'bayan ritaya, inda ya tattauna batun wahalhalun da ke cikin yaki da Boko Haram da tsaro.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com