Shiri Ya Baci: 'Yan Bindiga Sun Hallaka Jami'an Tsaro a Zamfara

Shiri Ya Baci: 'Yan Bindiga Sun Hallaka Jami'an Tsaro a Zamfara

  • An samu asarar rayukan jami'an tsaro na kungiyar 'yan sa-kai ta CJTF a jihar Zamfara da ke yankin Arewa maso Yammacin Najeriya
  • Jami'an tsaron sun rasa rayukansu yayin wata arangama da suka yi da tsagerun 'yan bindiga a karamar hukumar Tsafe
  • Lamarin ya auku ne makonni bayan wasu 'yan bindiga sun hallaka masallata a yankin lokacin Sallar Asuba

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Zamfara - 'Yan bindiga sun hallaka 'yan sa-kai na CJTF akalla guda takwas a jihar Zamfara.

'Yan sa-kan na CJTF sun rasa rayukansu ne a harin da ‘yan bindiga suka kai a kauyen Dan Loto, da ke karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.

'Yan bindiga sun hallaka 'yan sa-kai a Zamfara
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal. Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Jaridar Daily Trust ta kawo rahoto cewa mambobin CJTF sun faɗa tarkon ‘yan bindiga ne a lokacin da suke amsa kiran gaggawa kan yunƙurin maharan na kawo hari ga al’umma.

Kara karanta wannan

Ana batun zargin kisan Kiristoci, yan bindiga sun yi ta'asa a masallacin Katsina

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Harin ya faru ne kusan makonni biyu bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a masallaci, inda suka kashe mutane biyar ciki har da limami a yankin.

Ƙauyen Dan Loto na cikin Yandoton Daji, inda aka kashe waɗannan masallata a ranar 26 ga watan Satumba, 2025.

Yadda 'yan bindiga suka kashe jami'an CJTF

Wani mazaunin yankin mai suna Usman Yusuf Tsafe ya tabbatar da cewa an kashe mambobin na CJTF yayin musayar wuta da ‘yan bindigan.

"Mai yiwuwa ‘yan bindigan sun samu labarin zuwan ‘yan sa-kan ne, shi ya sa suka yi musu kwanton-bauna."
“Sun kashe su sannan suka gudu zuwa cikin daji. Ba su kai hari ga mazauna kauyen ba, sun yi niyyar farmakar jami'an CJTF din ne kawai."

- Usman Yusuf Tsafe

Mutanen Zamfara sun firgita saboda harin

Wani mazaunin Yandoton Daji, mai suna Aliyu Danlami, ya bayyana cewa al’ummar yankin sun shiga fargaba da rudani bayan harin.

Kara karanta wannan

Sojoji sun samu gagarumar nasara kan 'yan bindiga a Sokoto

“An tattaro gawarwakin waɗanda aka kashe daga wurin harin kuma an binne su bisa tanadin da addinin Musulunci ya yi."
“Mutanen kauyen sun firgita ƙwarai, amma sun yi sa’a ba a kai hari ga al’umma ko sace kowa ba."

- Aliyu Danlami

Karanta karin wasu labaran kan 'yan bindiga

'Yan bindiga sun sace mutane a Zamfara

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu 'yan bindiga dauke da makamai, sun yi awon gaba da mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba a jihar Zamfara.

'Yan bindigan sun sace mutane 30 yayin wani hari da suka kai a kauyen Zamfarawa, da ke gundumar Zugu cikin karamar hukumar Bukkuyum ta jihar Zamfara.

Miyagun 'yan bindigan sun yi dirar mikiya a kauyen kafin daga bisani su bude wuta kan mai uwa da wabi.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng