2026: An Saki Jerin Jami'o'i 50 Mafi Nagarta a Najeriya, BUK da ABU Sun Fafata

2026: An Saki Jerin Jami'o'i 50 Mafi Nagarta a Najeriya, BUK da ABU Sun Fafata

  • Rahoto ya ce Jami’ar Ibadan ta zama jami’a mafi nagarta a Najeriya a jadawalin Times Higher Education na shekarar 2026
  • Jami’ar ta koma kan gaba daga matsayi na hudu a 2025, inda ta doke jami'ar Covenant da ta yi nasara a 2024 da 2025
  • Jadawalin ya nuna cewa jami’o’i 50 ne daga Najeriya da suka shiga cikin jadawalin, ciki har da jami'o'in BUK da ABU Zariya

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja – Jami’ar Ibadan (UI) na kan kololuwar jadawalin mujallar Times Higher Education (THE) a 2026, inda ta zama jami’a mafi daraja a Najeriya.

An wallafa rahoton ne a ranar Alhamis, inda aka nuna cewa jami’ar Ibadan ta samu matsayi tsakanin 801 zuwa 1,000 a duniya.

Jami'o'in Najeriya, ABU, BUK da IU
Wasu daga cikin jami'o'in da suka yi fice a Najeriya. Hoto: ABU Zaria|Bayero University Kano|University of Ibadan
Source: Facebook

A sakon da aka wallafa a shafin mujallar, an bayyana cewa jami'ar BUK da ABU Zariya na cikin wadanda suka taka rawa a bana.

Kara karanta wannan

Abin da Mahmood Yakubu ya fadawa Tinubu a takardar ajiye shugabancin INEC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matakan tantance jami'o'in duniya

Rahoton ya bayyana cewa jami’ar Ibadan ta samu nasarar zama mafi daraja ne bayan tantance jami’o’i 2,191 daga ƙasashe 115 a fadin duniya.

An kimanta jami’o’in ne bisa fannoni biyar: yanayin koyarwa, muhalli da ingancin kayan bincike, hulɗa da masana’antu da gogayya a duniya.

Jami'ar jihar Gombe
Wani sashe na jami'ar jihar Gombe. Hoto: MSSN Gombe State University
Source: UGC

Jami’o’in da suka biyo baya a Najeriya

A jadawalin shekarar 2026, Jami’ar Legas (UNILAG) ta zo ta biyu, Jami’ar Bayero (BUK) ta zo ta uku.

BUK ta samu karramawa a matsayin jami’ar da ta fi kwarewa wajen hulɗar ƙasa da ƙasa, yayin da Jami'ar Covenant ta yi fice a fannin hulɗar masana’antu da kasuwanci.

Jerin jami'o'in da suka yi fice a Najeriya:

1. Jami’ar Ibadan

2. Jami’ar Legas

3. Jami’ar Bayero, Kano

4. Jami’ar Covenant

5. Jami’ar Landmark

6. Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya

7. Jami’ar Fasaha ta Tarayya, Minna

8. Jami’ar Ilorin

9. Jami’ar Jos

10. Jami’ar Najeriya, Nsukka

Kara karanta wannan

Jam'iyyar ADC ta kafa sharuda 4 kafin ba 'yan siyasa tikitin takara a 2027

11. Jami’ar Babcock

12. Jami’ar jihar Delta, Abraka

13. Jami’ar jihar Ekiti

14. Jami’ar Aikin Noma ta Tarayya, Abeokuta

15. Jami’ar Fasaha ta Tarayya, Akure

16. Jami’ar Fasaha ta Tarayya, Owerri

17. Jami’ar Tarayya, Oye-Ekiti

18. Jami’ar Fasaha ta Ladoke Akintola

19. Jami’ar jihar Legas

20. Jami’ar Nnamdi Azikiwe

21. Jami’ar Obafemi Awolowo

22. Jami’ar Binin

23. Jami’ar Kalaba

24. Jami’ar Fatakwal

25. Jami’ar Admiralty ta Najeriya

26. Jami’ar jihar Akwa Ibom

27. Jami’ar Al-Hikmah

28. Jami’ar Augustine

29. Jami’ar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta Bamidele Olumilua, Ikere-Ekiti

30. Jami’ar jihar Bauchi, Gadau

31. Jami’ar Likitanci ta jihar Bayelsa

32. Jami’ar Baze

33. Jami’ar Fasaha ta Bells

34. Jami’ar Bowen

35. Jami’ar Evangel, Akaeze

36. Jami’ar Tarayya, Lafiya

37. Jami’ar Albarkatun Man Fetur ta Tarayya, Effurun

38. Jami’ar Fountain

39. Jami’ar Godfrey Okoye

40. Jami’ar Igbinedion, Okada

41. Jami’ar jihar Kaduna

42. Jami’ar Ilimi ta jihar Legas

43. Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta jihar Legas

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun sace matar babban jami'in gwamnati, suna neman miliyoyin Naira

44. Jami’ar Lead City

45. Jami’ar Maryam Abacha American ta Najeriya

46. Jami’ar jihar Nasarawa, Keffi

47. Jami’ar Redeemer’s

48. Jami’ar jihar Rivers

49. Jami’ar Thomas Adewumi

50. Jami’ar jihar Cross River

Jami'o'in Najeriya za su fara yajin aiki

A wani rahoton, kun ji cewa kungiyar malaman jami'a a Najeriya, ASUU ta fara shirin tafiya yajin aiki.

Rahotanni sun nuna cewa kungiyar za ta fara yajin aiki ne saboda wasu hakkokinsu da suka ce an gaza biya.

Gwamnatin tarayya ta fara maganar shawo kan malaman domin kaucewa rufe jami'o'i amma suna cewa ba ja da baya idan ba a biya su ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng