Gwamna Zulum Ya Gwangwaje 'Yar Kabilar Igbo da Kyautar Ban Mamaki a Borno
- Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya faranta ran wata ma'aikaciyar lafiya 'yar asalin Anambra
- Mai girma Zulum ya ba matar gida a jihar Borno tare da ba danta wurin da zai rika aiki ba tare da bata lokaci ba
- Matar 'yar kabilar Igbo ta yi godiya ga gwamnan inda ta nuna cewa ya saba yi mata abubuwa na alheri
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Borno - Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya ba wata ma’aikaciyar lafiya, Mrs. Marbel Ijeoma Duaka, ‘yar asalin jihar Anambra, kyautar gida.
Gwamna Zulum ya ba ta kyuatar gidan ne mai dakuna biyu wanda aka sanyawa kayan daki.

Source: Facebook
Gwamna Zulum ya ba Ibo kyautar gida
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun bakin gwamnan, Dauda Iliya, ya sanya a shafinsa na Facebook.
A cewar sanarwar, Gwamna Zulum ya mika mata makullin gidan ne a ranar Talata, 7 ga watan Oktoban 2025.
Haka kuma, ɗanta Anthony, wanda ya kammala karatu a fannin banki da harkokin kudi, ya samu aiki a jami’ar jihar Borno mai suna Kashim Ibrahim da ke Maiduguri.
Gwamna Zulum ya bayyana cewa Marbel Ijeoma Duaka ta yi aiki a asibitin ta Mafa fiye da shekaru 20 ba tare da ta taɓa barin garin ba, ko a lokacin da ake tsananin rikicin Boko Haram.
"Ta yi aiki a nan sama da shekaru 24, ba ta bar Mafa ko da na wata guda ba. A lokacin rikicin Boko Haram, mutane da dama sun gudu daga garin, amma ita ta zauna, duk da cewa ba ‘yar asalin jihar bace.”
"Ta taɓa kula da yawancin ‘yan uwana, har ma da mahaifiyata."
"Za a sanya sunanki a jikin takardar mallakar gidan. Kada ki bar Mafa, har bayan kin yi ritaya.”
"Za a ba danki, Anthony, aiki a jami'ar Kashim Ibrahim da ke Maiduguri. Aikinsa zai fara ne nan take."
- Gwamna Babagana Umara Zulum
Marbel Ijeoma Duaka na daga cikin malamai da ma’aikatan lafiya 72 da suka karɓi sababbin gidaje a bikin da aka gudanar a karamar hukumar Mafa a ranar Talata.

Source: Facebook
'Yar kabilar Ibon ta yi godiya
Da take mayar da martani, Marbel Ijeoma Duaka ta bayyana cewa wannan rana ita ce mafi farin ciki a rayuwarta.
"Yau rana ce ta farin ciki a gare ni, saboda Mai girma Gwamna ya girmama ni kuma ya yaba da aikina a Mafa. Ya kasance mai kirki a gareni.”
"Ya ba ni gurbin yin karatun digiri na farko, yanzu kuma ya ba ɗana aiki, sannan ya ba ni gida. Ina matukar godiya."
- Marbel Ijeoma Duaka
Gwamnatin Zulum ta raba tallafi a Borno
A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya raba tallafin kayan abinci kyauta ga jama'a.
Gwamna Zulum ya bada tallafin ne ga mutum 18,000 a garin Dikwa da ke yankin tsakiyar jihar Borno.

Kara karanta wannan
An taso gwamna a Arewa a gaba ya koma APC, Tinubu zai iya karasa aikin da Buhari ya watsar
Zulum ya ce matakin raba kayan tallafin ya zama dole domin guje wa kalubalen yunwa da wadanda suka rasa amfanin gona ka iya shiga nan gaba a yankin.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

