Gwamnatin Kano Ta Fara Binciken Ganduje, an Jero Zunuban da Ake Tuhumarsa da Su

Gwamnatin Kano Ta Fara Binciken Ganduje, an Jero Zunuban da Ake Tuhumarsa da Su

  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Kano, PCACC ta fara binciken Abdullahi Umar Ganduje
  • Ana zargin Ganduje bisa zargin karkatar da sama da Naira biliyan huɗu zuwa aikin tashar tsandauri na Dala da ke jihar
  • Rahotanni sun nuna cewa an cire hannun gwamnatin Kano daga cikin masu mallakar kamfanin, inda ’ya’yan Ganduje suka rike mukaman daraktoci

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Bayan zargin karkatar da makudan biliyoyi a aikin tashar tsandauri a Dala, an fara binciken Abdullahi Umar Ganduje.

Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Kano (PCACC) ta tabbatar da fara bincike kan tsohon gwamnan Kano domin gano bakin zaren.

Gwamnatin Kano ta fara binciken Ganduje kan zargin badalaka
Gwamna Abba Kabir da Abdullahi Umar Ganduje. Hoto: Abba Kabir Yusuf, Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Source: Facebook

Rahoton Aminiya ya bayyana cewa sama da Naira biliyan huɗu ne ake zargin an karkatar zuwa aikin ta hanyar kwangila da aka bayar.

Kara karanta wannan

'Ka ba mu dama': Mutanen Sokoto sun tura sako ga Tinubu kan harin ƴan bindiga

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda wasu ke ganin zarge-zarge kan Ganduje

Majiyoyi sun ce an gano yadda aka mayar da wani kaso na kuɗin mallakar jihar zuwa ga iyalan tsohon gwamnan a shekarar 2020.

Saboda haka ne gwamnatin jihar ta rasa mallakar kamfanin, inda aka maye gurbin ’ya’yan Abdullahi Ganduje a matsayin daraktoci da masu hannun jari.

Wannan bincike da aka ya sake jawo maganganu kan yadda ake zargin gwamnatin Ganduje da karkatar da makudan kudi a Kano.

Duk da haka wasu na ganin bita da kulli ne na siyasa domin fakewa da zarge-zargen tsohuwar gwamnati da ake ganin ba abin da ya kamata a yanzu ba kenan.

Musabbabin binciken Ganduje kan zargin badakala

Shugaban hukumar, Saidu Yahya, ya tabbatar da cewa binciken ya samo asali ne daga koke-koken jama’a kan zargin karkatar da kuɗin jihar.

Ya bayyana cewa hukumar ta riga ta gayyaci wasu da ake zargi da hannu a lamarin, inda aka kama mutum ɗaya kuma aka sake shi bisa beli.

Kara karanta wannan

Sokoto: Ƴan bindiga sun tilasta mutane barin gidajensu, garuruwa 17 sun zama kufai

Ana zargin Ganduje da iyalansa da badakalar N4bn
Tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje. Hoto: Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Source: Twitter

Abubuwan da binciken ya bankado kan Ganduje

Binciken ya kuma gano cewa wani daga cikin wadanda ake zargi yanzu yana zaune a Yola, Jihar Adamawa, kuma ana sa ran cafke shi nan kusa.

Saidu Yahya ya ce hukumar za ta kai shari’ar kotu da zarar ta kammala bincike domin akwai isassun shaidu da za su tabbatar da zargin, cewar TheCable.

“Bincikenmu ya kusa zuwa ƙarshe kuma za mu tabbatar an yi adalci ga jama’ar Kano bisa wannan zargi.”

- Saidu Yahya

Lamarin ya sake janyo cece-kuce a Kano, inda jama’a ke kira ga gwamnati da ta tabbatar da gaskiya da bin doka a wannan batu.

Kungiyoyi sun taso Ganduje a gaba

A baya, mun ba ku labarin cewa shugaban jam'iyyar APC, Abdullahi Ganduje ya shiga wata matsala bayan an bukaci EFCC ta cafke shi kan cin hanci.

Kungiyoyin yaki da cin hanci sun shigar da korafi kan EFCC domin daukar mataki kan tsohon gwamnan Kano game da zarge-zargen.

Kara karanta wannan

Rashin imani: Yadda harin 'yan bindiga ya maida wani gari zuwa kufai a Kwara

Hakan na zuwa ne yayin da ake zargin Ganduje da badakalar makudan kudi lokacin da yake mulkin Kano daga 2015 zuwa 2023.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.