Dubu Ta Cika: An Kama Matashin da Ake Zargi da Sace Basarake a Kano, Ya Fara Kiran Sunaye

Dubu Ta Cika: An Kama Matashin da Ake Zargi da Sace Basarake a Kano, Ya Fara Kiran Sunaye

  • Yan sanda sun kama matashi dan shekara 27 da ake zargi da hannu a garkuwa da Dagacin Garun Babba a shekarar 2023
  • Matashin wanda aka fi sani da Yellow ya amsa cewa su suka sace basaraken, ya fara jero sunayen duka masu hannu a lamarin
  • Rundunar Yan Sandan Kano ta tabbatar da cewa za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Bayan tsawon shekaru biyu da faruwar lamarin, 'yan sanda sun cafke wanda ake zargi da hannu a garkuwa da Dagacin Garun Babba, Alhaji Abdulmumini Mudi Zakari.

Rundunar ‘Yan Sanda ta Kano ta tabbatar da kama wani matashi mai shekara 27 , Usman Lawan Baba, wanda aka fi sani da “Yellow”, bisa zargin hannu a sace basaraken a 2023.

Kara karanta wannan

Bayan yi wa matar Sarki tsirara, an kama mutum 10 da zargin yunƙurin hallaka basarake

SP Abdullahi Haruna Kiyawa.
Hoton kakakin rundunar yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa. Hoto: Abdullahi Haruna Kiyawa
Source: Facebook

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar. Kamar yadda Leadership ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yan sanda sun kama wanda ya sace basarake

Ya bayyana cewa an cafke wanda ake zargi ne a ranar 2 ga Oktoba, 2025 a garin Dakatsalle, karamar hukumar Bebeji ta Jihar Kano, bayan shekaru biyu da aikata laifin.

“An kama shi ne bisa zargin hannu a garkuwa da mutane da kuma fashi da makami da ya kunshi Dagacin Garun Babba, wanda ya faru a ranar 9 ga Agusta, 2023,” in ji sanarwar.

Idan ba ku manta ba, miyagu sun yi garkuwa da basaraken tare da sace masa kudi har ₦2,750,000, wayar Tecno Kevo 4 da agogo, kafin jami’an 'yan sanda su ceto shi.

SP Abdullahi Kiyawa ya ce wanda ake zargi ya amsa laifinsa, inda ya bayyana cewa ya samu ₦6,000 a matsayin rabonsa daga abin da suka sace.

Kara karanta wannan

Abin Fashewa ya tarwatse a tsakiyar kananan yara a cikin birnin Kano, ya yi barna

Yellow ya jero sunayen masu hannu a lamarin

Haka kuma ya fallasa sunayen wasu abokan aikinsa, ciki har da wadanda aka kashe a samamen ‘yan sanda da kuma wadanda suke hannun hukuma.

Sanarwar ta kara da cewa:

“Wanda aka kama, Usman Lawan Baba, ya amsa laifin tare da bayyana sunayen abokan harkallarsa, wadanda suka hada da: Bello Kici-Kici na kauyen Falgore, wanda yan sanda suka kashe a samame.
“Mallam Sale na karamar hukumar Gezawa, wanda shi ma aka kashe yayin wani fashi da makami. Shehu Ruwa na kauyen Gafan, wanda ke gidan gyaran hali bisa wani laifi na garkuwa da mutane.
Sauran sun hada da Ibrahim Gwanja, Sule Naye da wani mutum da ba a bayyana sunansa ba, wadanda ake ci gaba da bincike a kansu.”
Jami'an yan sanda.
Hoton dakarun Rundunar Yan Sandan Najeriya a bakin aiki. Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Rundunar ta tabbatar da cewa za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala bincike, cewar rahoton Punch.

Kwalbar barkonon tsohuwa ta fashe a Kano

Kara karanta wannan

Fusatattun matasa sun kona gidan basarake a Binuwai, sun bayyana dalilinsu

A wani labarin, kun ji cewa kwalbar barkonon tsohuwada yan sanda ke amfani da ita ta fashe a hannun yara a yankin Sharada, cikin birnin Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa yara hudu yan gida daya sun ji raunuka sakamakon fashewar kwalbar a unguwar Bakin Kwata da ke Sharada.

Tuni dai yan sanda suka kai dauki wurin da lamarin ya faru, tare da killace shi domin tabbatar da babu sauran abubuwa masu hadari.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262