Bayan Shafe Shekaru Yana Koyar da Alkur'ani a Masallacin Annabi SAW, Sheikh Bashir Ya Rasu

Bayan Shafe Shekaru Yana Koyar da Alkur'ani a Masallacin Annabi SAW, Sheikh Bashir Ya Rasu

  • Sheikh Bashir bin Ahmed Siddiq, malamin da ke koyar da Alkur'ani a masallacin Annabi S.A.W a Madina ya riga mu gidan gaskiya
  • Hukumomin kasar Saudiyya sun tabbatar da rasuwar babban malamin, wanda ya shafe sama da shekaru 60 yana koyar wa a masallacin Annabi
  • A sanarwar da Saudiyya ta fitar, ta ce Sheikh Bashir ya shafe kusan duka rayuwarsa wajen koyar da Alkur'ani Mai Girma a Madina

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Madina, Saudi Arabia - Musulmi sun yi babban rashi da aka tabbatar da rasuwar daya daga cikin manyan malaman da ke koyar da Alkur'ani a masallacin Annabi SAW da ke Madina.

Rahotanni daga kasar Saudiyya sun tabbatar da cewa Sheikh Bashir bin Ahmed Siddiq, ya riga mu gidan gaskiya a yau Laraba, 1 ga watan Oktoba, 2025.

Kara karanta wannan

'Tattali da tsaro,' Bangarori 23 da Tinubu ya tabo a jawabinsa na ranar 'yanci

Sheikh Bashir bin Ahmed Siddiq.
Hoton Marigayi Sheikh Bashir bin Ahmed Siddiq. Hoto: Inside The Haramain
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da hukumar kula da manyan masallatai biyu masu alfarma da ke Makkah da Madina ta wallafa a shafinta Inside The Haramain na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sheikh Bashir bin Ahmed ya rasu a Madina

Sheikh Bashir na ɗaya daga cikin manyan malamai masu koyar da Alƙur’ani Mai Girma da karatunsa a Masallacin Manzon Allah (SAW) da ke birnin Madina.

Sanarwar ta ce:

"InnalilLahi wa inna ilaihi raji'un, daya daga cikin manyan malamai masu koyar da Alƙur’ani Mai Girma da karatunsa a Masallacin Manzon Allah (SAW) a Madina, Sheikh Bashir bin Ahmed Siddiq, ya rasu a yau Laraba."

Sheikh Bashir ya sadaukar da kusan shekaru 60 na rayuwarsa wajen koyar da Alƙur’ani a Masallacin Annabi, inda dubban ɗalibai suka yi karatu a ƙarƙashinsa.

Manyan malaman da Sheikh Bashir ya koyar

Daga cikin fitattun ɗaliban da marigayin ya koyar akwai:

  • Sheikh Muhammad Ayyoub da Sheikh Ali Jaber – tsofaffin limaman manyan masallatar biyu masu alfarma (Allah ya jikansu da rahama).
  • Sheikh Muhammad Al-Mukhtar Al-Shanqiti – mamba a Majalisar Manyan Malamai ta kasar Saudiyya.
  • Sheikh Abdul Muhsin Al-Qasim da Sheikh Salah Al-Budair – limaman yanzu na Masallacin Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad SAW da ke Madina.

Kara karanta wannan

'Yan Boko Haram sun yi ta'addanci a Borno, an kona fadar basarake, an kashe mutane

Marigayi Sheikh Bashir ya kasance mutum mai tawali'u, wanda ake daukarsa a matsayin ginshiƙi wajen ilimin Alƙur’ani a Masallacin Annabi.

Marigayi Sheikh Bashir Bin Ahmed Siddiqi.
Hoton babban malamin Alkur'ani a masallacin Annabi Muhammad SAW, Sheikh Bashir bin Ahmed Siddiqi. Hoto: Inside The Haramain
Source: Facebook

Shehin Malamin ya bar gadon ilimi da ɗalibai da ke ci gaba da hidimar Alƙur’ani a fadin duniya ta Musulunci.

"Allah Maɗaukaki Ya ji kansa, Ya karɓi kyawawan ayyukanda hidimarsa ga Alƙur’ani Mai Girma ta tsawon shekaru, ya kuma ɗaukaka matsayinsa tare da salihan bayi," in ji sanarwar.

Babban Mufti na Saudiyya ya kwanta dama

A wani labarin, kun ji cewa Saudiyya ta sanar da rasuwar babban mufti na ƙasar, Sheikh Abdulaziz bin Abdullah Al Sheikh, yana da shekara 82 a duniya.

Kafin rasuwarsa, Sheikh Al Sheikh ya rike mukaman da suka haɗa da babban mufti na Saudiyya, shugaban Majalisar Manyan Malamai, da kuma shugaban hukumar bincike da bayar da fatawa.

Sarki Salman da Yarima Mohammed bin Salman sun mika ta’aziyarsu ga iyalan marigayin, al’ummar Saudiyya da kuma musulmin duniya baki ɗaya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262