An Hallaka Shedanin Dan Bindiga, Matasa Sun Kona Fadar Sarki da Harsashi Ya Samu Dalibai

An Hallaka Shedanin Dan Bindiga, Matasa Sun Kona Fadar Sarki da Harsashi Ya Samu Dalibai

  • Sojojin Operation Whirl Stroke sun yi nasara kan wani kasurgumin dan ta'adda wanda ya sheka barzahu yayin arangama
  • Dakarun sojojin sun kashe ɗan fashi a Jato-Aka, amma harbin bazata ya rutsa da ɗalibai uku, ɗaya mace wacce ta rasu
  • Lamarin ya tayar da zanga-zanga a garin Jato-Aka, matasa sun fito tituna suka ƙone ofishin mai sarautar gargajiya, Mue Ter

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Makurdi, Benue – Sojojin Operation Whirl Stroke sun kashe wani da ake zargin ɗan bindiga ne a lokacin artabu da suka yi.

Lamarin ya faru ne a Jato-Aka, ƙaramar hukumar Kwande a jihar Benue a ranar Talata 30 ga watan Satumbar 2025.

An harbe tantirin dan bindiga a Benue
Dakarun sojoji yayin sintiri a Najeriya da Gwamna Alia Hyacinth. Hoto: Fr. Alia Iormen Hyacinth.
Source: Facebook

Shedanin dan bindiga ya bakunci lahira

Rahoton Zagazola Makama ya tabbatar da cewa harbin ya wuce inda ya rutsa da ɗalibai uku, inda ɗaya daga cikinsu ta rasa ranta.

Kara karanta wannan

'Tattali da tsaro,' Bangarori 23 da Tinubu ya tabo a jawabinsa na ranar 'yanci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyi sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:20 na rana, lokacin da sojojin ke sintiri a yankin.

An ce rikicin ya fara ne bayan da suka hango wasu da ake zargi ’yan bindiga ne a kan babur suna ɗauke da makamai.

A cewar wani shaidar gani da ido, ’yan bindigar ne suka fara bude wuta bayan ganin sojojin.

Sojojin sun mayar da martani, inda aka harbe ɗaya daga cikin su har lahira, sauran kuma suka tsere suka bar baburansu.

Dalibar makaranta ta mutu bayan harbin bindiga

Sai dai a lokacin, wasu ɗaliban makarantar sakandaren kimiyya ta gwamnati da ke Jato-Aka da suke dawowa, sun ci karo da harbin ba tsammani.

Wata ɗaliba mace daga cikinsu daga baya an tabbatar da mutuwarta a asibitin NKST, yayin da sauran biyun ke karɓar magani.

Rundunar sojoji ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa sojojin kawai sun kare kansu ne bayan an bude musu wuta.

Kara karanta wannan

Za a shiga kotu da gwamna bayan kisan 'malami' da ya je yi masa wa'azi har gida

Sojoji sun yi ajalin wani dan bindiga a Benue
Taswirar jihar Benue da ke Arewa ta Tsakiyar Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Matakin da matasa suka dauka a Benue

Rahotanni sun nuna cewa labarin rasuwar ɗalibar ya tayar da tarzoma a garin Jato-Aka, inda fusatattun matasa suka yi zanga-zanga tare da ƙone ofishin mai sarautar gargajiya na yankin, Mue Ter.

Rundunar ’yan sanda ta tabbatar da aukuwar lamarin, tana mai cewa an jibge jami’an yan sanda a garin don dawo da zaman lafiya.

Ta kara da cewa an kwantar da tarzoma, sai dai ana ci gaba da sintiri don hana sake tashin rikici.

Hukumomi sun roki al’ummar Jato-Aka da su kwantar da hankali su kuma yi aiki tare da jami’an tsaro yayin da ake ci gaba da bincike.

An kashe dan bindiga bayan ya tuba

Mun ba ku labarin cewa an kama mutum daya bisa zargin hannu a kisan wani tsohon dan bindiga da ya tuba a yankin Zaki-Biam, jihar Benue.

Rahotanni sun ce tsohon dan bindigan ya rasa ransa ne bayan wasu mutane sun bi shi a babur sun harbe shi ba tare da bata lokaci ba.

Kara karanta wannan

Asiri ya tonu: Dakarun sojoji sun cafke masu hada baki da 'yan ta'adda a Katsina

Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa tana ci gaba da bincike domin kama sauran wadanda suka gudu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.