Za a Sheka Ruwan Sama da Iska Mai Karfi a Taraba, Zamfara da Wasu Jihohin Arewa

Za a Sheka Ruwan Sama da Iska Mai Karfi a Taraba, Zamfara da Wasu Jihohin Arewa

  • NiMet ta yi hasashen ruwan sama da iska mai karfi zai sauka a a sassa daban-daban na Najeriya, musamman a Kudancin kasar
  • Ebonyi, Cross River, Akwa Ibom, Enugu, Imo da Abia na cikin haɗarin ambaliya, inda aka bukaci jama'a su dauki matakan kariya
  • NiMet ta gargadi direbobi su yi taka tsantsan yayin ruwan sama saboda matsalar ganin hanya da santsin titi da ka iya jawo haɗurra

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Hukumar kula da yanayi ta kasa (NiMet) ta fitar da sabon hasashen yanayi da zai yi aiki a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025.

A cikin sabon hasahsen, NiMet ta ce akwai yiwuwar za a samu ruwan sama da iska mai karfi, hade da tsawa a sassa da dama na Najeriya.

Hukumar NiMet ta ce akwai yiwuwar a sheka ruwan sama a ranar Laraba a wasu jihohi
Ruwan sama da iska mai karfi na sauka a wasu sassan Najeriya. Hoto: Sani Hamza/Staff
Source: Original

Rahoton da NiMet ta wallafa a shafinta na X a daren ranar 30 ga Satumba, 2025 ya nuna cewa ruwan zai iya jawo cikas ga harkokin jama'a na yau da kullum.

Kara karanta wannan

Abubuwa 4 da ya kamata jam'iyyar ADC ta yi don kayar da Tinubu, APC a zaben 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hasashen ruwan sama a jihohin Arewa

A cewar rahoton, da safiyar Laraba, za a wayi gari da yanayi na rana tare da hadari, amma akwai yiwuwar a samu ruwan sama a wasu sassan Taraba da kudancin Adamawa.

Rahoton ya kara da cewa za a samu hadari da bullar rana a safiyar Laraba a sassan Abuja da jihohin Arewa ta tsakiyar Najeriya.

Sannan wasu sassan babban birnin tarayya, Neja, Kogi, Kwara da Nasarawa za su iya samun ruwan sama da iska mai karfi a safiyar ranar.

Da yamma kuma, ruwan sama da iska mai matsakaicin karfi za su shafi kudancin Zamfara, kudancin Kaduna, kudancin Bauchi, Kebbi, kudancin Gombe da kuma Taraba.

A Arewa ta Tsakiya ma, ana hasashen ruwan sama mai karfi zai sauka a mafi yawan jihohin shiyyar, abin da zai iya kawo tangarda ga zirga-zirgar jama’a da kuma ayyukan kasuwanci.

Kara karanta wannan

An shigar da 'yan sanda kotu, za a fara shari'a kan takaita hawa babur a Gombe

Hasashen ruwan sama a Kudancin Najeriya

A kudancin kasar kuwa, rahoton ya nuna cewa za a iya samun yanayi na hadari da ruwan sama lokaci zuwa lokaci a safiyar Laraba a jihohin Edo, Legas, Delta, Ogun, Ondo, Enugu, Imo, Ebonyi, Ribas, Cross River, Akwa Ibom da Bayelsa.

Da yammacin ranar kuma, ana sa ran ruwan sama da iska mai karfi a yawancin jihohin Kudancin Najeriya.

Nimet ta bukaci masu ababen hawa su yi hattara yayin tuki ana ruwa saboda fargabar hadurra
Wasu masu ababen hawa na tuki a kan titi yayin da ake sheka ruwan sama. Hoto: Getty Images
Source: UGC

Gargadi daga NiMet ga 'yan Najeriya

Hukumar NiMet ta yi gargadin yiwuwar ambaliyar ruwa a jihohin Ebonyi, Cross River, Akwa Ibom, Enugu, Imo da Abia.

Haka kuma, an shawarci direbobi da su yi tuki a hankali saboda ruwan sama mai karfi na rage hangen nesa, kuma titi na santsi, wanda zai iya jawo ambaliya.

An shawarci mazauna yankunan da aka yi hasashen za su samu ambaliya da su dauki matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyinsu.

Kaduna: Ambaliya ta lalata gidaje, gonaki

Kara karanta wannan

Tsautsayi: Yadda 'Dan sanda ya harbe kansa har lahira a Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa, ambaliyar ruwa ta lalata gidaje da gonaki a garin Manchok, da ke masarautar Moro’a a karamar hukar Kaura ta jihar Kaduna.

Mazauna yankin wadanda suka rasa kayayyakin gida da amfanin gona, sun nemi agajin gaggawa daga wajen gwamnati.

Lamarin wanda ya jawo asarar dukiya da amfanin gona, ya sanya mazaunan yankin sun mika kokon bararsu yayin da suke jimamin asarar da suka tafka.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com