Shugaba Tinubu Ya Hadu da Kwankwaso Gaba da Gaba, An ga Abin da Ya Faru a Bidiyo

Shugaba Tinubu Ya Hadu da Kwankwaso Gaba da Gaba, An ga Abin da Ya Faru a Bidiyo

  • A yau Juma'a, 26 ga watan Satumba, 2025 aka gudanar da bikin nadin sabon Sarkin Ibadan, Oba Rashidi Ladoja a dakin taro na Mapo Hall
  • Manyan baki ciki har da Mai Girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da jagoran NNPP na kasa, Dr. Rabi'u Kwankwaso sun halarci bikin
  • Kwankwaso, wanda ake rade-radin zai sauya sheka zuwa jam'iyyar APC, ya hadu da Bola Tinubu a wurin kuma sun gaisa cikin fara'a

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ibadan, jihar Oyo - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya hadu da manyan jiga-jigan 'yan siyasa na jam'iyyu daban-daban a bikin nadin Olubadan na 44 a jihar Oyo.

Daya daga cikin wadanda Tinubu ya hadu da su kuma suka gaisa akwai tsohon dan takarar shugaban kasa kuma jagoran jam'iyyar NNPP na kasa, Rabi'u Musa Kwankwaso.

Kara karanta wannan

Sarki ya kinkimo bukatar kirkiro jiha 1, ya fadawa Tinubu gaba da gaba a Ibadan

Shugaba Tinubu da Kwankwaso.
Hoton Shugaba Bola Tinubu a gidan gwamnati da jagoran NNPP, Rabiu Kwankwaso Hoto: @OfficialABAT, @RMKwankwaso
Source: Facebook

Mai taimaka wa shugaban kasa na musamman kan harkokin kafafen sada zumunta, Dada Olusegun ne ya tabbatar da hakan a wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bola Tinubu ya gaisa da Kwankwaso a Ibadan

A bidiyon, an ga lokacin da Kwankwaso ya karasa wurin da Shugaba Tinubu yake tsaye kuma ya mika masa hannu suka gaisa tare da musayar kalaman gaisuwa.

Dada Olusegun ya ce:

"Mai Girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gaisa da tsofaffin gwamnoni, Olagunsoye Oyinlola, Rabiu Kwankwaso da Ibikunle Amosun (a wurin bikin nadin Olubadan na 44)."

Ana rade-radin Kwankwaso zai shiga APC

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake rade-radin Kwankwaso ya shirya sauya sheka daga jam'iyyar NNPP zuwa APC mai mulkin Najeriya.

Lamarin dai ya ja hankalin 'yan siyasa musamman a jihar Kano, inda Kwankwaso ke da tarin magoya baya da kuma 'yan adawa.

A kwanakin baya, Kwankwaso ya fito da kansa ya ce zai iya komawa APC amma bisa sharudda, ba haka nan zai kama ya koma jam'iyyar ba.

Kara karanta wannan

Magana ta kare, tsohon gwamna ya zama Sarki mai martaba a Najeriya

A cewarsa, ko da zai koma APC sai an zauna an fada masa yadda za a yi da mutanensa na NNPP da za su biyo shi a dukkan sassan Najeriya.

Wannan ya kara rura wutar jita-jitar cewa tsohon gwamnan na iya komawa APC kowa ne lokaci, musamman da wani labari ya fara yawo cewa ya fara tattaunawa da shugaban jam'iyyar, Farfesa Nentawe Yilwatda.

Dr. Rabiu Musa Kwankwaso.
Hoton dan takarar NNPP a zaben shugaban kasar 2023, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso
Source: Facebook

Kwankwaso ya musanta tattaunawa da APC

Sai dai Kwankwaso ya fito ya karyata wannan labari a shafinsa na Facebook, yana mai tabbatar da cewa babu wata jam'iyya da ya cimma yarjejeniyar shiga a yanzu.

Ana cikin haka ne, Shugaba Tinubu wanda shi ne jagoran APC ya hadu da Kwanwkaso, kuma fadar shugaban kasa ta wallafa bidiyon gaisawar da jagororin biyu suka yi a Ibadan.

NNPP ta yi bayani kan shirin Kwankwaso

A wani labarin, kun ji cewa jam’iyyar NNPP, ta musanta jita-jitar da ake yadawa cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yanke shawarar shiga APC.

Shugaban NNPP na kasa, Ajuji Ahmed, ya ce ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2023, ba zai sauya sheka zuwa APC mai mulki ba.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun bude wuta a masallaci ranar Juma'a, mutane da dama sun mutu

A baya dai Kwankwaso ya bayyana cewa jam’iyyarsa a buɗe take ga shiga jam’iyyar APC, amma sai an zaune a tattake wuri.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262