'Yan Bindiga Sun Bi Dare, Sun Bude Wuta a Gidan Babban Malami a Jihar Nasarawa

'Yan Bindiga Sun Bi Dare, Sun Bude Wuta a Gidan Babban Malami a Jihar Nasarawa

  • 'Yan bindiga sun bude wuta yayin da suka kai hari gidan malamin addini a garin Agyaragu a karamar hukumar Obi ta jihar Nasarawa
  • 'Yan ta'addan sun yi awon gaba da matar faston, Patience Nasamu da bakuwa, sun bar jariri dan watanni uku a tsakar gida
  • Fasto Nasamu ya tabbatar da aukuwar lamarin, ya ce lokacin da 'yan bindigar suka whiga gidan, yana coci wurin yiwa wani addu'ar neman lafiya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Nasarawa - Wasu ’yan bindiga sun sace Matar Fasto Samuel Nasamu na Cocin Word of God Church da ke Agyaragu a ƙaramar hukumar Obi, Jihar Nasarawa.

Rahotanni sun nuna cewa matar babban malamin addinin mai suna, Misis Patience Nasamu ta shiga hannun yan bindiga ne lokacin da suka farmaki gidan da take zaune.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun sace basarake tare da wasu mata a Plateau

Jihar Nasarawa.
Hoton taswirar jihar Nasarawa a Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Rahoton Leadership ya nuna cewa bayan matar malamin, maharan sun kuma hada da wata dalibarsa da ta kai ziyara gidan, sun yi awon gaba da su zuwa cikin jeji.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai ’yan bindigar sun bar jaririn faston mai watanni uku da haihuwa a gidan, abin da ya jefa garin gaba ɗaya cikin firgici.

Yan bindiga sun bude wuta a gidan malami

Shaidu sun ce maharan sun dira gidan faston ne da misalin ƙarfe 8:15 na dare, ranar Lahadi, inda suka tilasta wa matar ta buɗe musu ƙofa bayan sun yi ta harbe-harbe a sama.

Fasto Nasamu, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, ya bayyana cewa 'yan bindigar sun yi ƙoƙarin karya tagogi da ƙofofin gidan da guduma, amma ba su iya shigowa ba saboda ƙarfin kariya.

Ya ce lamarin ya faru ne jim kaɗan bayan kammala ibadar cocin, lokacin da ya fita ya yi wa wani mamba mai rashin lafiya addu’a.

Kara karanta wannan

Ana sulhu da 'yan ta'adda a Katsina, 'yan bindiga sun sace hakimi da wasu mata 2 a Filato

Yadda aka sace matar fasto da bakuwarsa

“Ina cikin addu’a ga daya daga cikin dalibai na masu zuwa coci wanda ke fama da rashin lafiya sai matata ta kira ni.
"Abin da kawai na ji daga gare ta shi ne addu’a, ko bayyana abin da ke faruwa ba ta iya ba. Da na iso gida, sai na tarar an sace ita da baƙuwar da ta zo garemu, an bar jaririnmu a nan,” in ji shi.
Jami'an 'yan sanda.
Hoton dakarun 'yan sandaa bakin aiki Hoto: @PoliceNG
Source: Getty Images

Faston ya ƙara da cewa jami’an rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa sun ziyarci wurin domin tantance lamarin da kuma daukar matakin da ya dace.

Duk da haka, malamin ya ce har yanzu masu garkuwar ba su tuntubi iyalansa domin neman kuɗin fansa ba, in ji rahoton PM News.

'Yan bindiga sun sace dan siyasa a Kaduna

A wani labarin, kun ji cewa wasu miyagun 'yan bindiga sun farmaki kauyuka biyu a kananan hukumomin Kudan da Makarfi da ke cikin jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi wa jami'an tsaro kwanton bauna, an samu asarar rayuka

Yayin wadannan hare-hare da aka kai kusan lokci guda, maharan sun sace mutum uku ciki har da wani sanannen dan siyasa a yankin.

Majiyoyi sun bayyana cewa maharan sun afka wa mutane da dare, ba tare da tsammani ba, inda suka bude wuta a iska don tsorata jama'a.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262