Gwamnatin Sokoto Ta Bude Shafin Daukar Matasa 3,000 Aiki, Ana Bukatar Takardu 4

Gwamnatin Sokoto Ta Bude Shafin Daukar Matasa 3,000 Aiki, Ana Bukatar Takardu 4

  • Gwamnatin Sokoto ta sanar da bude shafin daukar matasa 3,000 masu kwalin NCE, HND da Digiri aiki a ma'aikatu daban daban
  • Za a fara daukar ma’aikatan ne daga yau Litinin, 22 ga Satumba, 2025, kuma za a rufe shafin daukar aikin a ranar 6 ga Oktoba, 2025
  • Kwamitin daukar ma'aikatan Sokoto, ya bayyana takardun da ake bukata don neman aikin da suka hada da takardar haihuwa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Sokoto - Gwamnatin Sokoto ta sanar da cewa za ta fara daukar sababbin ma’aikata daga ranar Litinin, 22 ga Satumba, har zuwa 6 ga Oktoba, 2025.

Sakataren kwamitin daukar ma’aikata, Barista Gandi Muhammad, ya ce an kaddamar da shirin ne domin ba matasan jihar damar samun aiki a ma’aikatun gwamnati.

Gwamna Ahmad Aliyu ya amince a dauki matasa 3,000 aiki a Sokoto.
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, zaune a dakin taro da ke gidan gwamnati. Hoto: @Ahmedaliyuskt
Source: Facebook

An bude shafin daukar aiki a Sokoto

Kara karanta wannan

Sabuwar cuta mai cin naman jiki ta bulla a Adamawa, gwamnati ta fara bincike

Jaridar Punch ta rahoto Barista Gandi yana cewa wadanda suka cancanta za su iya karɓar fom kyauta daga ƙaramar hukumarsu, kafin daga bisani su cike fom ɗin a shafin yanar gizo: employment.sokotostate.gov.ng

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gandi Muhammad ya ce dole ne masu masu neman aikin su yi rajista da adireshin imel da lambar wayarsu na gaskiya, su kuma shigar da takardu masu inganci.

Takardun da ake bukata sun haɗa da shaidar kammala makaranta, takardar asalin ɗan ƙasa, takardar haihuwa, da lambar NIN. Za a kuma buƙaci ɗaukar hoton fasfo kai tsaye yayin cikewa.

Ya jaddada cewa cike fom da na yanar gizo kyauta ne gaba ɗaya, sannan duk wanda ya yi kuskuren cike fom din sau biyu zai iya rasa damar samun aikin.

Gwamnati ta ba matasan Sokoto shawara

Kwamitin ya bayyana cewa za a rika tura sakonni kai tsaye ta imel ko sakon kartakwana ga wadanda suka cancanta.

Ya bayyana cewa ta imel, ko shafin yanar gizo ne kawai wadanda suka cancanta za su ga sakon wucewa mataki na gaba, ko kiran tattaunawa.

Haka kuma, an gargadi jama’a da su guji biyan kowa wani kuɗi domin neman aikin, kwamitin yana mai cewa za a dauki ma'aikatan ne bisa cancanta.

Kara karanta wannan

Sakkwato: Shugabannin makarantun sakandare 6 sun tsunduma kansu a matsala

“Muna kira ga matasa da su yi amfani da wannan dama domin samun aikin gwamnati cikin sauki, kuma bisa gaskiya da adalci."

- Barr. Gandi Muhammad.

An bukaci matasan Sokoto su nemi aikin gwamnatin jihar a ma'aikatu daban daban.
Taswirar jihar Sokoto da ke a Arewa maso Yammacin Najeriya. Hoto: Legit.ng
Source: Original

Matasa 3,000 za a ba aiki a Sokoto

Mai magana da yawun gidan gwamnati, Mallam Abubakar Bawa, ya bayyana cewa Gwamna Ahmed Aliyu ya amince da daukar ma’aikata 3,000 daga ƙananan hukumomi 23 na jihar.

Gwamnan ya ce shirin zai rage zaman banza, ya kuma ƙarfafa ma’aikatun gwamnati da suka shafi lafiya, ilimi, da sauran fannoni na ci gaban jama’a, inji Premium Times.

Ya ce matasa masu NCE, HND ko digiri za su fi samun dama a shirin, domin gwamnati tana da niyyar mayar da hankali wajen ba su ayyukan da za su ciyar da jihar gaba.

Gwamna Fintiri zai dauki matasa aiki

A wani labarin, mun ruwaito cewa, gwamnatin jihar Adamawa za ta dauki matasa 12,000 aiki kafin Disambar 2025 domin yaki da rashin aikin yi.

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri ne ya bayyana hakan a yayin ganawarsa da kungiyar kiristoci mata ta WOWICAN, a ziyarar da suka kai ofishinsa.

Kara karanta wannan

'Yan fansho sun fusata, suna shirin fara zanga zanga tsirara a fadin Najeriya

Gwamnan ya shaidawa kungiyar cewa gwamnatinsa ta daura damarar kafa tubalin ci gaba a ilimi, lafiya da sauransu ga kowane dan Adamawa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com