Bayan Rasuwarta, Shugaba Tinubu Ya Tuna ’Ya’yan Marigayiya, Ya ba Su Aiki a Abuja

Bayan Rasuwarta, Shugaba Tinubu Ya Tuna ’Ya’yan Marigayiya, Ya ba Su Aiki a Abuja

  • Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin bai wa ’ya’yan marigayiya tsohuwar shugabar ma'aikata a Abuja aiki
  • Tinubu ya dauki wannan matakin ne domin tallafawa rayuwar iyalan marigayiyar, Grace Adayilo da ta rasu a Abuja
  • Minista Nyesom Wike ya bayyana Adayilo a matsayin mai gaskiya, jajirtacciya, mai tawali’u da biyayya ga aikinta

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya bayyana kokarin Bola Tinubu bayan rasuwar tsohuwar shugabar ma'aikata a Abuja.

Wike ya ce Bola Tinubu ya bayar da umarnin daukar ’ya’yan marigayiya Grace Adayilo aiki nan take a birnin tarayya Abuja.

Tinubu ya ba 'ya'yan tsohuwar shugabar ma'aikata a Abuja aiki
Bola Tinubu yayin rattaba hannu kan wata doka a Abuja. Hoto; Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Facebook

Sanarwar ta fito ne daga cocin 'National Christian Centre' yayin jana’izar Adayilo, wacce ta rasu a ranar 1 ga Satumba, 2025, cewar rahoton Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yaushe marigayiya Grace ta rasu?

Kara karanta wannan

2007: PDP ta bukaci Tinubu ya fara shirin mika mulki, ta kawo dalili

Marigayiyar kafin rasuwarta, ita ce mace kuma 'yar asalin babban birnin tarayya da Shugaba Bola Tinubu ya nada shugabar ma'aikatan hukumar FCTA.

Wata majiya daga hukumar raya babban birnin tarayya (FCTA), ta ce Grace Adayilo ta rasu ne a safiyar Litinin, 1 ga Satumba, 2025.

A ranar Alhamis din makon jiya ne aka yi wa Grace Adayilo ganin karshe, lokacin da ta wakilci Nyesom Wike a wani taron 'yan G7.

Taimakon da Tinubu ya yi wa iyalan marigayiyar

Wike ya ce matakin ya zama dole domin tallafawa iyalanta bayan rasuwarta a matsayin mai kula da su, tare da yabawa marigayiyar.

Ya ce:

"Dukkanmu mun sani wata rana za mu mutu, wannan tabbas babu kwana-kwana amma wasu daga cikin mutuwa da ake yi idan suka faru, dole za a ji zafi sosai."

Wike ya ce mutuwarta ta fi ciwo saboda ba ta nuna wata alama ba; an gan ta a aiki yau, gobe kuma labarin mutuwa ya iso.

Wike ya isa da umarnin Tinubu game da ba 'ya'yan Grace aiki a Abuja
Tsohon gwamnan Rivers, Nyesom Wike a PortHarcourt. Hoto: Nyesom Wike.
Source: Facebook

Wike ya fadi gudunmawar marigayiyar a Abuja

Wike ya bayyana yadda ya fara haduwa da ita bayan nadin babban sakatare, matsayin da Tinubu ya kirkiro domin inganta harkokin aikin gwamnati.

Kara karanta wannan

ADC ta fadi gwamnan da doka ta yarje wa Tinubu ya sauke daga kujerarsa

"Na ce ina son mutum wanda ya ke da jajircewa da mutunta aiki, mutum mai kan-kan da kai da kuma wanda zai yi biyayyar aiki.
"Shugaban kasa ya umarce ni da na ba 'ya'yan marigayiyar guda hudu aiki nan take saboda Tinubu ya fahimci cewa a yanzu babu mai rike iyalinta."

- Nyesom Wike

Ya kara cewa Adayilo ba ta yi wasa da albashi ko hakkokin ma’aikata ba, tana kammala ayyuka cikin gaggawa, kuma uwa nagari ce ga kowa.

Ministan ya kuma bayyana cewa Adayilo tana da kwarewa a siyasa da iya hada kan jama’arta fiye da yadda aka sani.

Tinubu ya kaddamar da aiki a masallaci

Mun ba ku labarin cewa yayin ziyara a jihar Kaduna, Bola Tinubu ya kaddamar da wasu ayyuka a masallacin Sultan Bello da ke jihar Kaduna.

An gina sabon wurin alwala mai cin mutane 300 da bandaki 50 na zamani a babban masallacin da ke jihar.

Tinubu ya kaddamar da wadannan ayyuka na zamani wanda kamfanin Tantita ya yi a masallacin inda ya yaba da wannan aiki.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.