Safarar Ƙwaya: Yadda Ƴan Najeriya 3 Suka Tsira daga Hukuncin Kisa a Saudiyya

Safarar Ƙwaya: Yadda Ƴan Najeriya 3 Suka Tsira daga Hukuncin Kisa a Saudiyya

  • Mahajjatan Najeriya uku sun samu ‘yanci daga Saudiyya bayan makonni huɗu a tsare bayan da aka zarge su da safarar kwayoyi
  • An gano cewa wata ƙungiyar masu safarar kwayoyi ce ta sanya kwayoyi a jakunkunan mahajjatan a filin jirgin saman Kano
  • Bayan samun rahoton, Shugaba Bola Tinubu ya ba da umarnin a tattauna da hukumomin Saudiyya, lamarin da ya kai ga an sako su

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Wasu mahajjatan Najeriya uku, sun tsira daga hukuncin kisa, bayan da aka tsare su makonni hudu a Saudiyya, bisa zargin safarar kwayoyi.

Mutanen sun samu 'yanci biyo bayan tattaunawa tsakanin hukumar NDLEA da hukumar yaki da sha da fataucin kwayoyi ta Saudiyya (GDNC).

Saudiyya ta sako 'yan Najeriya 3 da aka tsare su bisa zargin safarar kwayoyi.
Hoton wata mata 'yar kabilar Oromo sanye da nikabi a cikin kasuwar Amhara, Habasha. Hoto: Eric Lafforgue/Art in All of Us A kula: An yi amfani da hoton ne kawai don buga misali.
Source: Getty Images

Sunayen 'yan Najeriya da Saudiyya ta saki

Rahoton BBC Hausa ya nuna cewa, alhazan Najeriya ukun da aka saki bayan makonni huɗu a tsare sune:

Kara karanta wannan

Ribas: Peter Obi ya zargi gwamnatin Najeriya da yi wa dimokuradiyya kisan mummuke

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

  • Hajiya Maryam Hussain Abdullahi daga jihar Jigawa
  • Hajiya Abdullahi Bahijja daga jihar Kano
  • Malam Abdulhamid Saddieq daga jihar Jigawa

Hukumar NDLEA ce ta tabbatar da sakin mahajjatan a taron manema labarai da aka gudanar a Abuja ranar Laraba, 17 ga Satumba, 2025.

Mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi, ya bayyana cewa wata kungiyar masu safarar miyagun kwayoyi a filin jirgin saman Kano ce ta sanya kwayoyi a jakunkunan mahajjatan ba tare da saninsu ba.

Ya ce an sanya kwayoyi a kayan mutanen ne lokacin da za su je yin Umrah ta jirgin Ethiopian Airlines ET940 daga Kano zuwa Jiddih a ranar 6 ga Agusta, inda aka kama su bayan saukarsu.

Bincike ya fallasa masu safarar kwaya

Shugaban NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (ritaya), ya umarci gudanar da cikakken bincike bayan iyalan mahajjatan sun kai koke game da kama 'yan uwansu.

Wannan bincike ya kai ga cafke shugaban ƙungiyar masu safarar kwayoyin, Mohammed Ali Abubakar wanda aka fi sani da Bello Karama, tare da wasu abokan harkallarsa uku ciki har da ma’aikatan jirgi.

Kara karanta wannan

NAHCON ta nuna damuwa, Sheikh Pakistan ya hango matsalar da za a iya samu a Hajjin 2026

Wadanda aka kama tare da Bello Karama akwai Celestina Emmanuel Yayock, Abdulbasit Adamu Sagagi, da Jazuli Kabir, kuma an riga an gurfanar da su gaban kotu, inji rahoton Punch.

Tinubu ya taimaka aka sako mahajjatan 3

Bayan samun shaidu da ke tabbatar da cewa mahajjatan Najeriyar ba su da laifi, Buba Marwa ya shiga tattaunawa kai tsaye da hukumomin Saudiyya, musamman hukumar GDNC.

Wannan mataki ya samu cikakkan goyon baya daga Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ya ce ba za a bar wani ɗan Najeriya ya sha wahala a ƙasar waje saboda abin da bai aikata ba.

An rahoto cewa, Saudiyya ta sako daya daga cikin mahajjatan a ranar Lahadi, yayin da aka sako sauran biyun a ranar Litinin.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa ya ce Tinubu ne ya sanya baki aka sako 'yan Najeriya da aka tsare a Saudiyya.
Shugaban hukumar NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa, yana jawabi a ofishinsa a Abuja. Hoto: @ndlea_nigeria
Source: Facebook

Hukuncin sha da safarar kwayoyi a Saudiyya

Dokar Saudiyya kan yaki da miyagun kwayoyi, wadda aka kafa bisa umarnin sarki mai lamba 4/B/966, ta raba hukunci tsakanin masu safarar miyagun kwayoyi, masu fatauci, da masu amfani da su.

1. Masu fataucin miyagun kwayoyi

Hukunci mafi tsauri ga mutanen da ke da hannu wajen safarar miyagun kwayoyi da shigar da su cikin kasar Saudiyya shi ne kisa, cewar rahoton shafin gwamnatin Saudiyya.

Kara karanta wannan

Jagoran 'yan bindiga ya fara cika alkawari kan yarjejeniyar sulhu a Katsina

Mutumin da ya shigo da miyagun kwayoyi daga waje ana daukarsa a matsayin "fataken miyagun kwayoyi," haka shi ma mutumin da ya karbi miyagun kwayoyi ya raba wa masu sayarwa.

2. Masu dillacin miyagun kwayoyi

Dokar miyagun kwayoyi ta bambanta tsakanin mutumin da ya fara dillacin miyagun kwayoyi a karon farko da kuma wanda aka riga aka hukunta a baya.

Ga wanda ya fara aikata laifin a karon farko, hukuncin dauri ne, ko bulala, ko tara, ko kuma dukkan su. Amma ga wanda ya maimaita laifin, ana kara masa hukunci kuma za a iya yanke masa hukuncin kisa.

3. Masu amfani da miyagun kwayoyi

Alkali na yanke ya masu tu'ammali da miyagun kwayoyi hukuncin daurin shekaru biyu kuma ana hukunta shi bisa shari'a.

Idan mai laifin ɗan ƙasar waje ne, ana korarsa shi daga kasar. Sannan mai tu'ammali da kwaya amma yana zuwa wajen likita don ya daina, ana kai shi asibitin da aka kebe don gyara tarbiyar masu shaye shaye.

Dokar Saudiyya, bisa ga shawarar Majalisar Dinkin Duniya, tana ɗaukar masu amfani da miyagun kwayoyi a matsayin majinyata da suke buƙatar kulawar likita.

Kara karanta wannan

Saudiyya ta sako maniyyatan Najeriya da aka tsare kan zargin safarar kwayoyi

Saudiyya ta cafke Maryam Hussaini

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Saudiyya ta cafke Maryam Hussaini Abdullahi, ‘yar Kano, bisa zarginta da mallakar wata jaka da aka samu tabar wiwi a ciki.

Abdullahi Baffa, mijin Maryam, ya zargi kamfanin jiragen Ethiopian Airlines da sauya jakunkuna, da ya jawo aka danganta sunan matarsa da jakar da ba tata ba.

Ya roƙi gwamnatin Najeriya ta taimaka wajen tabbatar da gaskiya, ciki har da buƙatar a duba bidiyon CCTV a filin jirgin Kano don wanke mai dakinsa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com