Manyan 'Yan Siyasa 4 da Za Su Koma Bakin Aiki bayan Janye Dokar Ta Baci a Rivers

Manyan 'Yan Siyasa 4 da Za Su Koma Bakin Aiki bayan Janye Dokar Ta Baci a Rivers

  • Shugaba Bola Tinubu ya sanar da dawowar gwamnatin Siminalayi Fubara bayan karewar watanni shida na dokar ta-baci a Rivers
  • Janye dokar ta bacin na nufin, Fubara, mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu da wasu shugabannin siyasa za su koma bakin aiki
  • Tinubu ya yi kira ga shugabanni su guje wa rikici, ya ce dimokuraɗiyya za ta yi nasara ne kawai cikin zaman lafiya da haɗin kai

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja – Bayan tsawon watanni shida, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da ƙarewar dokar ta-baci da ya sanya a jihar Rivers.

Shugaban kasar na Najeriya ya bayyana cewa, gwamnatin Siminalayi Fubara ce yanzu za ta ci gaba da tafiyar da al’ammuran Rivers.

Bayan janye dokar ta baci a Rivers, Tinubu ya mayar da gwamna, mataimakinsa da 'yan majalisa bakin aiki
Shugaba Bola Tinubu ya gana da Siminalayi Fubara, Nyesom Wike da wasu kusoshin Rivers a Abuja. Hoto: @SimFubaraKSC
Source: Facebook

Tinubu ya janye dokar ta baci a Rivers

A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Laraba, 17 ga Satumba, Shugaba Tinubu ya ce:

Kara karanta wannan

Rivers: Ƴan majalisa sun dauki matakin farko bayan Tinubu ya janye dokar ta baci

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“Ina mai farin cikin sanar da ku cewa dokar ta-baci a jihar Rivers za ta zo ƙarshe daga ƙarfe 12 na daren yau (Laraba).

Sanarwar, ta tabbatar da cewa manyan ‘yan siyasa da aka dakatar a lokacin dokar ta-bacin za su koma kujerunsu.

Shugabannin siyasa 4 da za su koma aiki

Legit Hausa ta zakulo manyan shugabannin siyasar Rivers da za su koma kan kujerunsu bayan sanarwar Tinubu, su ne:

1. Gwamna Siminalayi Fubara

Gwamna Siminalayi Fubara, zai koma kan kujerarsa bayan dakatar da shi da Tinubu ya yi na tsawon watanni shida.

Tinubu ya ce rikicin da ya shiga tsakanin gwamnan da majalisar dokokin jihar ya durƙusar da harkokin mulki, wanda ya sa aka dauki mataki na ayyana dokar, amma yanzu, bayan karewar wa'adinta, Fubara zai koma ofis.

2. Mataimakiyar gwamna, Ngozi Odu

Ita ma mataimakiyar gwamnan jihar Rivers, Ngozi Nma Odu za ta koma kujerarta ta ci gaba da mulki, kamar Fubara.

Kara karanta wannan

Atiku ya yi nazari, ya gano abin da yake tunanin ya hana kawar da 'yan bindiga a Najeriya

Shugaban ƙasa ya bayyana cewa dawo da jagorancin gwamnati zai dawo da kwanciyar hankali da daidaito a jihar Rivers.

3. Kakakin majalisar jiha, Amaewhule

Martins Amaewhule, kakakin majalisar dokokin jihar, na cikin manyan shugabannin siyasa hudu da za su koma kan kujerarsu.

Tinubu ya ce yana fatan kakakin majalisar zai zama ginshiƙi wajen daidaita dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisar jihar.

4. Mambobin majalisar dokokin Rivers

Dukkanin mambobin majalisar dokokin jihar Rivers da aka dakatar a lokacin dokar ta-baci za su koma bakin aiki.

Shugaba Tinubu ya tunatar da su muhimmancin yin haɗin kai da gwamnati domin samar da zaman lafiya da ci gaban jihar.

Shugaba Bola Tinubu ya ce yana fatan za a samu ci gaba mai dorewa a jihar Rivers bayan karewar dokar ta baci.
Shugaba Bola Tinubu yana jawabi a taron FEC, da Gwamna Siminalayi Fubara yana gabatar da kasafi a majalisar Rivers. Hoto: @aonanuga1956, @SimFubaraKSC
Source: Twitter

Tinubu ya yi gargadi da jan kunne

Shugaban ƙasa ya yi amfani da wannan dama wajen tunatar da shugabannin siyasa a fadin ƙasa cewa:

“Za mu iya kawo al’ummarmu ribar dimokuraɗiyya ne kawai idan muna cikin yanayin zaman lafiya, bin tsari a gudanar da kyakkyawan mulki.”

Ya kuma kira gwamnoni da majalisun dokoki a faɗin ƙasar da su koyi darasi daga rikicin Rivers tare da guje wa rikicin da zai rushe gwamnatinsu.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya fadi dalilin janye dokar ta baci a Rivers

Rivers: Dalilin kawo karshen dokar ta-baci

Tun da fari, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Tinubu ya sanar da kawo ƙarshen dokar ta-baci da ya ayyana a jihar Rivers a watan Maris din 2025.

Tinubu ya ce ya janye dokar ne yanzu saboda ya samu kwarin gwiwa daga sababbin al’amura da suka nuna alamar sulhu da shirin shugabannin jihar Rivers na komawa tafiyar da mulki ta hanyar dimokuraɗiyya.

A sanarwar da ya fitar a ranar Laraba, shugaban kasar ya ce babu dalilin ci gaba da dokar ta-baci a jihar bayan tsawon watanni shida da na ayyana ta.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com