Sardauna: Gwamna Ya Karrama Ahmadu Bello, Ya Yi Alƙawarin ci Gaba da Yaɗa Manufofinsa

Sardauna: Gwamna Ya Karrama Ahmadu Bello, Ya Yi Alƙawarin ci Gaba da Yaɗa Manufofinsa

  • Gwamnan Kwara AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana aniyarsa ta ci gaba da yada manufofin marigayi Sardaunan Sokoto, Ahmadu Bello
  • Gwamnan ya yabawa Bola Tinubu kan gyare-gyaren tattalin arziki da ci gaban jihohi, sannan ya jaddada shirin daukar jami'an tsaron gandun daji don kare dazuzzuka
  • Shugaban GAMA, Mohammed Tunde Akanbi, ya bayyana goyon baya ga gwamna tare da yabawa ayyukan ci gaba da sake suna fadar gwamnati 'Ahmadu Bello House'

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ilorin, Kwara - Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya sha alwashin ci gaba da ayyukan alheri.

Gwamnan ya ce zai ci gaba yada manufofi na marigayi Firimiyan Arewa, Sir Ahmadu Bello domin kawo sauyi.

Gwamnan Kwara ya karrama marigayi Sardauna
Gwamnan Kwara, AbdulRahman AbdulRazak da Sardaunan Sokoto. Hoto: Kwara State Government.
Source: Facebook

Gwamna ya yabawa kungiyar Gamji da mutunta Sardauna

AbdulRazaq, wanda shi ne Sardaunan Ilorin, ya bayyana haka ne lokacin da shugabannin kungiyar Gamji Members Association (GAMA) suka kai masa ziyara a Ilorin, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Sulhu ya kankama, gwamna ya kawo shirin da za a tallafawa tubabbun 'yan bindiga

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya gode wa kungiyar bisa yadda suka ci gaba da rike ruhin Gamji, inda ya shawarce su da ka da su daina jajircewa wajen aikin cigaba.

Ya ce:

“Yana da muhimmanci mu ci gaba da yada abin da marigayi Sardaunan Sakkwato ya tsaya a kai, mu karkatar da albarkatunmu ga ci gaba.”

Ya kuma shawarci shugabannin GAMA su kafa reshen matasa don tabbatar da dorewar ayyukan kungiyar a nan gaba, tare da goyon bayansa na musamman.

AbdulRazaq ya yi karin haske kan irin tallafin da yake baiwa GAMA, inda ya tabbatar musu cewa zai ci gaba da tsayawa tare da su.

Gwamnan ya yaba da Shugaba Bola Tinubu bisa gyare-gyaren tattalin arziki da shirye-shiryen ci gaba, yana mai cewa jihohi suna amfana sosai daga tsarin.

“Akwai manyan cigaba a jihohi, yanzu ana biyan albashi akan lokaci, har ma kananan hukumomi suna kaddamar da ayyukan gina tituna."

- AbdulRahman AbdulRazaq

Kara karanta wannan

Mutuwa mai yankar kauna: Matashin dan siyasa, Yunusa Yusuf ya rasu a Abuja

Gwamnan Kwara ya yaba da manufofin Sardaunan Sokoto
Taswirar jihar Kwara da ke Arewa ta Tsakiyar Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

Gwamna ya yi alkawari kan rashin tsaro

Kan batun tsaro, ya ce matsalar tana wucewa, inda ya bayyana shirin daukar jami'an tsaron gandun daji don hana ’yan ta’adda mamaye dazuzzukan jihar.

Gwamnan ya jaddada muhimmancin aikin rijistar masu kada kuri’a, inda ya bukaci kungiyar da sauran jama’a su karfafa wa mutane yin rajista.

Tun da farko, Shugaban GAMA, Alhaji Mohammed Tunde Akanbi, ya bayyana goyon bayan kungiyar ga gwamna bisa salon shugabanci da ya dace da na Sardauna.

Akanbi ya jinjinawa gwamna saboda sake sunan fadar gwamnatin jihar zuwa 'Ahmadu Bello House', a matsayin shaida ta gaskiyar biyayyarsa ga Sardauna.

Mambobin tawagar GAMA da suka raka shi sun hada da Alhaji Saadu Salahu, Dr Ghali Alaaya, Engr Usman Baba Jibril, da sauran fitattun ’yan kungiyar.

Gwamna ya maka tsohon dan majalisa a kotu

Kun ji cewa gwamnan jihar Kwara ya maka Moshood Mustapha da ɗan'uwansa a kotu bisa zargin tayar da zaune tsaye da yaɗa bidiyon ɓatanci.

Kara karanta wannan

Gwamna Uba Sani ya yi wa 'yan siyasa shagube, ya fadi bammbancinsa da su

An gurfanar da su be a ranar Litinin a Ilorin, ammma sun musanta tuhume-tuhumen, inda alkali ya bayar da su beli a kan N5m.

Tuhume-tuhumen sun haɗa da haɗin baki don ƙirƙira da yaɗa bidiyon ɓatanci, wanda zai iya tunzura jama'a kan gwamnan jihar.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.